• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Salon Yaki Da ‘Yan Ta’adda A Jihar Kaduna

by Shehu Yahaya
3 years ago
Kaduna

A kokarin da jami’an tsaro a Jihar Kaduna suke yi wajen magance ayyukan ‘yan ta’adda a fadin jihar, a karon farko kwamandan rundunar sojoji ta daya da ke jihar Manjo Janar Taoreed Lagbaja, ya jagoranci wata tawaga na jami’an soja domin kai farmaki a sansanin ‘yan ta’adda da ke garuruwa Buruku, Udawa, Manini, Birnin Gwari, Doka, Maganda, Kuyello da kuma Dogon Dawa duk shiyyar karamar hukumar Birnin Gwari na Jihar Kaduna.

Tawagar sun tarwatsa sansanin ‘yan ta’addan, inda suka kwato bindiga kirar AK47 da babura guda 18 da dunkulen harsashi na musamman guda 27 da kuma jikkata ‘yan ta’addan masu yawan gaske.

  • Malam Ina So A Taimaka Mun Da Maganin Damuwa Da Bakin Ciki?
  • Mace Za Ta Iya Yin Limancin Sallah?

Hakazalika, tawagan sun ceto wasu mutane uku da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a wani kauye mai suna Manini da ke Kan hanyar Birnin Gwari.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Birgediya Onyema Nwachukwu, ya raba wa manema labarai a Kaduna a ranar Litinin 30 ga watan Augustan 2022, ya ce bayan wani taho-mu-gama da sojojin suka yi da ‘yan ta’adda a dajin Birnin Gwari, sojoji sun jikkata ‘yan ta’adda da dama yayin da suka arce suka bar makamansu, lamarin da ya sanya suka kwato bindigogi da babura da kuma kubutar da mutane uku daga hannunsu.

A cewar rundunar sojan, sun kaddamar da kai samamen ne wuraran da ‘yan ta’addan suka yi sansani bisa jagoranci kwamadan rundunar, Manjo Janar Taoreed, tun daga ranar Alhamis na makon jiya har zuwa ranar Litinin na wannan makon, domin tabbatar da cewa an samu saukin kai hare-haren ‘yan ta’addan a Jihar Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Rundunar sojan ta bukaci al’ummar jihar musamman ma’aikatan kiwon lafiya da su sanya ido a kan duk wani mutum da zai zo neman agaji bisa samun rauni da ya yi, domin sanar da hukumomin tsaro

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
Labarai

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Next Post
Jakadan Sin Dake Nijeriya Ya Halarci Bikin Bude Ajin Horas Da Jami’an APC Ta Yanar Gizo

Jakadan Sin Dake Nijeriya Ya Halarci Bikin Bude Ajin Horas Da Jami’an APC Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.