ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
8 months ago
'Yan Bindiga

Duk da biliyoyin kudaden da gwamnatin tarayya ke warewa a kasafin kudi domin yaki da ta’addanci, yankunan Katsina, Sakkwato, Zamfara da Kebbi na ci-gaba da zama filin daga a yayin da ‘yan ta’adda ke ci-gaba da cin karensu ba babbaka da sabbin hare-hare.

 

Gagarumar matsalar wadda ta- ki- ci- ta- ki- cinyewa a tsayin shekaru kan yi sauki a wasu lokutan a wasu wuraren, haka ma hare- haren kan ci- gaba da ta’azzara tare da komawar murna a ciki ta yadda jama’a ba su da zabi face neman tsira da rai.

ADVERTISEMENT
  • Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da KuraAfuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da Kura

Yankin Arewa- Maso- Yammacin Nijeriya inda lamarin ya fi kamari na da iyaka da Jamhuriyar Nijar, kasar da ‘yan ta’adda ke amfani da makwabtakar suna shige da fice a tsakanin kasashen biyu domin tsira daga farmaki.

A yanzu haka yankuna da dama wadanda a baya ba su fuskanci kalubalen matsalar tsaro ba, a yanzu haka sun fara dandana ukubar ta’addanci da bakuntar sansanin gudun hijira.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A baya- bayan nan ‘yan ta’addan wadanda suka daura damarar hanawa al’umma kwanciyar hankali sun kashe daruruwan mutane, kona gidaje tare da garkuwa da mutane ciki har da mata da kananan yara.

Rahotanni daga yankunan sun tabbatar da yadda al’umma suka gaji suka kosa da jin alkawura marasa adadi daga gwamnati wadda ke kasa cikawa a yayin da hare-hare ke karuwa a duk shekara duk da karin kudaden tsaro da ake warewa..

A Sakkwato, kauyuka da dama kamar Giyawa, Kurawa, da Unguwar Lalle a gabascin Sakkwato hedikwatar gawurtaccen dan ta’adda Bello Turji sun fuskanci hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutane da dama a baya- bayan nan.

A Karamar Hukumar Sabon- Birni, wasu mazauna yankin sun tsere domin tsira da rai zuwa cikin dazuka bayan wani mummunan hari da ‘yan ta’addan suka kai a daren Lahadi.

A Zamfara, ‘yan bindiga sun kai hare-hare a Kauran- Namoda, Maradun da Dansadau da Shinkafi inda suka kashe manoma, aka dauki mutane fiye da 40, yayin da a Katsina, kauyuka kamar Batsari, Jibia da Kankara suka sake fuskantar luguden wuta, lamarin da ya tilasta mazauna barin gidajensu.

A cikin kasafin kudin 2025, gwamnatin tarayya ta ware fiye da Naira tiriliyan 3.2 domin yaki da matsalar tsaro, mafi girman kaso a cikin dukkan bangarorin gwamnati. Duk da haka, hare-haren suna karuwa, musamman a yankunan karkara da ba su da cikakken kariya.

Ba ya ga asarar rayuka, hare-haren sun durƙusar da tattalin arzikin yankunan. Gonaki sun lalace, sana’o’i sun tsaya, haka ma yawancin matasa sun fice daga kauyuka zuwa birane don neman mafaka.

A watannin da suka gabata daruruwan mutane ne suka kauracewa garuruwa da gidajen su tare da neman mafaka a wasu garuruwan domin tsira da rayukan su a yayin da garuwawan su suka zama lahira kusa.

A bayyane yake yadda barayin daji suka kassara ayyukan noma a Arewacin kasar nan ta hanyar tilastawa manoma biyan harajin amfanin gona, hana masu shuka da ma kone gonakin bakidaya lamarin da ya yi wa Arewa da kasa bakidaya mummunar illa wajen samar da wadataccen abinci.

A makon nan al’ummar jihar Zamfara sun fito fili sun bayyana yadda ‘yan ta’adda suka hana masu girbe amfanin gona a gonakin su. Mamoman sun bayyana cewar suna cikin fargabar yadda za su girbe tare da kwashe amfanin gonar su a yayin da damana ta kawo karshe.

Mamoman a karamar hukumar Shinkafi, sun bayyana cewar suna cikin zullumin ne a sakamakon hare- haren ‘yan bindiga a garuruwan su wanda ya sa suke cikin kunchi saboda rashin mafita.

A yayin da al’ummar ke neman agajin gaggawa daga wadanda lamarin ya shafa, gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewar ta na sane da halin da al’ummar Shinkafi ke ciki kuma za ta dauki matakan da suka kamata domin shawo kan matsalar wadda gwamnatin ta ce an samu nasara sosai kan barazanar barayin daji ga manoma a jihar.

Da yawa daga cikin mazauna yankunan da ‘yan ta’adda ke aika- aikarsu na ganin dabarun da hukumomin tsaro ke amfani da su ba su da inganci saboda rashin amfani da bayanan sirri daga al’umma da kuma jinkirin amsawa bayan kai hari.

Malam Aliyu Garba, wani manomi daga Giyawa, ya bayyana cewar “Ko da an ce gwamnati ta kara kudin tsaro, to ba mu ga bambanci ba. Idan har kudi ake kashewa haka, to ina sakamakon?”

Haka kuma, Lami Umar, wadda ta rasa danta a harin Maradun, ta ce “Mun gaji da alkawuran da ake yi mana na kawo karshen barayin daji ba tare da ganin sakamako ba.”

A kodayaushe Gwamnatocin Katisna, Sakkwato, Zamfara da Kebbi kan jaddada cewar suna aiki kafada da kafada da gwamnatin tarayya wajen yaki da ta’addanci da samar da zaman lafiya .

A wata sanarwa Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewar “Mun fara amfani da fasahar zamani wajen bibiyar hanyoyin ‘yan ta’adda, da kafa cibiyar bayanan sirri ta jiha wanda hakan zai taimaka wajen hana kai hare-hare.”

Sai dai masana na da ra’ayin karin kudin da ake kashewa a bangaren tsaro ba ya zama mafita idan ba a tabbatar da gaskiya, ingantaccen tsari da bin diddigin ayyukan hukumomin tsaro yadda ya kamata ba.

A kwanan nan al’ummar karamar hukumar Kebbe a jihar Sakkwato suka kokawa gwamnatin jiha da ta tarayya kan su kawo masu agajin gaggawa kan karuwar kisan gilla da ya shafi akalla garuruwa 12.

A jawabinsa a taron manema labarai, jagoran tawagar, Adamu Haruna Kebbe ya ce abin damuwa ne yawaitar karuwar hare- haren ta’addanci da ‘yan ta’addan ke yi masu wanda ya tilastawa daruruwan al’umma gudun hijira.

“Daruwan al’ummar mu sun bar garuruwan su, gidajen su, dukiyoynsu da gonakin su domin tsira da rai saboda jama’a na cikin fargaba saboda yanayin ya kazanta sosai, duk da hukumomi sun san abin da ke faruwa amma kisan gillar bai yi sauki ba.”

A kan wannan ya yi kira ga gwamnatin jihar Sakkwato da gwamnatin tarayya da su karfafawa hukumomin tsaro da kayan aiki domin shawo kan matsalar da ke hana masu bacci da idanu biyu.

Kebbe ya bayyana cewar al’ummar yankin sun yi gudun hijira daga mafi yawan garuruwan da lamarin ya shafa, ya ce rashin kawo agajin gaggawa zai sa matsalar tsaron ta kara tabarbarewa.

A kan wannan gagarumar matsalar tsaron, majalisar wakilai ta yi kira ga hukumomin tsaro da a matakin gaggawa su tura jami’an tsaro a mazabar tarayya ta Kebbe/Tambuwal domin shawo kan karuwar ayyukan ta’addanci a yankin.

Matakin majalisar ya biyo bayan amincewa da kudirin bukatar gaggawa da Honarabul Abdussamad Dasuki da ke wakiltar mazabar ya gabatar a zaman majalisar a ranar da ta gabata Talata kan yadda ‘yan ta’adda ke hanawa al’umma bacci da idanu biyu.

An samu yawaitar hare- haren ayyukan ta’addanci a Kebbe da Tambuwal, kisan al’umma da garkuwa da mutane da tarwatsa garuruwa da dama.

Al’ummar yankin sun bayyana cewar matsalar tsaron ta gurgunta tattalin arzikin yankin musamman ayyukan noma wanda ya sa daruruwan mutane da dama neman mafaka a sansanin gudun hijira a Sakkwato da makwabtan jihohi.

Dasuki ya bayyana cewar a ranar 12 ga Augusta 2025, ‘yan ta’adda sun shiga mazabar Fakku a karamar hukumar Kebbe tare da kashe mutane biyar da garkuwa da mutane 28 da satar shanu 37.

“Haka ma a ranar 15 ga Agusta barayin daji sun kai farmaki a mazabar Sangi tare da tilastawa jama’a neman mafaka a Kuchi da Koko a jihar Kebbi. Bugu da kari a ranar 18 ga Agusta ‘yan ta’adda sun afkawa mazabar Ungushi tare da kisan mutane biyu da garkuwa da mutane bakwai tare da asarar dabbobi.”

Dasuki ya kuma bayyana cewar, mazabar Jabo a karamar hukumar Tambuwal da mazabar Tambuwal/Shimfiri suna fuskantar kalubalen tsaro da ke bukatar agajin gaggawa.

Dan majalisar ya bayyana halin kuncin da al’ummar yankin ke ciki, ya ce munanan hare- haren sun tarwatsa kwanciyar hankalin al’umma, jama’a sun kauracewa garuruwa, haka ma yara sun daina zuwa makaranta, a yayin da manoma sun dakatar da zuwa gona a bisa ga tsoron ta’addancin.

A bisa ga amincewa da kudirin, majalisar ta bukaci rundunar sojin Nijeriya da rundunar ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta tura jami’an tsaro domin karfafa kai hare- hare a yankin Kuchi a karamar hukumar Kebbe da yankunan karamar hukumar Tambuwal domin kare rayuka, dukiyoyi da gonaki.

Wani mai sharhi a kan al’amurran yau da kullum Aliyu Daure Tambuwal ya bayyana cewar “Kasafin kudin sha’anin tsaro na karuwa a kowane kasafi, amma babu daidaito tsakanin abin da ake kashewa da sakamakon da ake gani. Ya ce sai an tunkari tushen matsalar, talauci, rashin aiki da cin hanci, sa’annan za a ga canji.”

Duk da karin kudin sha’anin tsaro da gwamnati ke warewa a kowace shekara, Arewa maso Yamma na ci- gaba da zama cibiyar ta’addanci ba kakkautawa ta yadda jama’a ke rayuwa a cikin tsoro, lamarin da ba za a ga canji ba matukar ba a tashi tsaye an yaki ta’addancin da zuciya daya ba.

'Yan Bindiga
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ posts Bio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato
'Yan Bindiga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.