ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

by Sani Anwar and Sulaiman
8 months ago
Tinubu

A makon da ya gabata ne, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi afuwa ga wasu daga cikin fursunoni na wannan kasa.

 

Jerin sunayen wadanda aka yi wa afuwar, wanda mai bai wa shugaban kasa shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar, sun hada da mutanen da aka yanke wa hukunci, kan laifuffuka daban-daban da suka hada da:

ADVERTISEMENT
  • Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
  • Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, masu safarar miyagun kwayoyi, ‘yan kasashen waje, Manjo Janar Mamman Batsa, Manjo Akubo, Farfesa Magaji Garba da sauran wadanda suka aikata manyan laifuka, irin su Maryam Sanda, Ken Saro Wiwa Ogoni su takwas, na daga cikin mutane 175 da shugaban kasar ya yi wa afuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya.

 

A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun rasu. Kazalika, kwamitin ya ba da shawarar yin afuwa ga fursunoni 82 tare da sassauta hukuncin dauri na fursunoni 65. Fursunonin bakwai da aka yanke wa hukuncin kisa, su ma sun shiga cikin jeren afuwar da shugaban kasar ya yi. Sannan, kwamitin ya ba da shawarar cewa; shugaban kasa ya mayar da hukuncin kisa zuwa daurin rai da rai.

 

Fagbemi ya gabatar da rahoton kwamitin a taron majalisar kasa, wanda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

 

A bangare guda kuma, ‘yan Nijeriya da dama na fadin albarkacin bakinsu, dangane da wannan afuwa da shugaban kasa ya yi wa masu laifukan daban-daban, wasu na da ra’ayin cewa; mafi yawan wadanda aka yi wa afuwar, ‘yan kwaya ne da rikakkun ‘yan ta’adda da kuma wadanda tuni suka mutu. A cikin masu nuna takaicin nasu; akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ‘yan siyasa, masu sharhi kan al’amuran yau da kullum, jam’iyyun adawa da kuma iyalai da sauran abokanan arziki da al’amarin ya shafa.

 

Iyalan marigayi Bilyaminu Ahmed Bello, na daya daga cikin wadanda suka bayyana rashin jin dadinsu, kan afuwar da shugaban kasa ya yi wa Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa bisa laifin kashe mijinta, wadanda suka bayyana yin afuwar a matsayin wani mummunan zalinci da aka tafka musu.

 

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin da ta gabata dauke da sa hannun Dakta Bello Haliru Mohammed (Dangaladiman Gwandu), a madadin ‘yan’uwa, ‘yan’uwan marigayin sun bayyana matakin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dauka na yi wa Sanda afuwa a matsayin wani mummunan sake fama musu raunukan da suka samu da kuma rashin adalci ga dan’uwan nasu.

 

Iyalan Bilyaminun sun bayyana cewa, sun ji matukar takaicin sakin Maryam da aka yi, inda suka bayyana hakan; a matsayin wani yunkuri na dadada wa danginta tare da yin watsi da bacin ran da ya addabi ‘yan’uwa da sauran abokan arzikin marigayin.

 

Maryam, mai shekaru 37, na daya daga cikin mutum 175 da aka yanke wa hukunci, aka kuma yi wa afuwa da jin kai a ranar Alhamis da ta gabata, a karkashin ikon shugaban kasa.

 

A bangare guda kuma, kwatsam! Sai ga sanarwar mahaifin mijin Maryam Sandan cewa; shi da kansa ne ya roki Shugaban Kasa Tinubu, ya yi wa sirikar tasa afuwa.

 

A cewarsa, ya dade yana neman rokon a yi wa Maryam sassauci tare da afuwa, wacce ke fuskantar hukuncin kisa, tun bayan yanke mata hukuncin da aka yi.

 

Alhaji Ahmed Bello Isa, wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta hadin gwiwa da aka yi da shi a ranar Talatar da ta gabata a Abuja tare da Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya bayyana cewa; dalilinsa na yin hakan, saboda tausayi tare kuma son ganin an sako masa surukarsa, domin ta samu ta kula da ‘ya’yanta guda biyu, domin kuwa, kashe ta ba zai taba dawo masa da dansa ba.

 

Ya kara da cewa, “Na yafe wa Maryam da aka samu da laifin kisan dana, kafin a kammala shari’a, na yi iya kokarina na sanar da ‘yansanda da kotu cewa; ba na so a gurfanar da ita a gaban kuliya, domin kuwa jikoki kamar yadda suka rasa mahaifinsu, haka nan kuma za su rasa mahaifiya.

 

“Na dauki wannan a matsayin iftila’i, wanda Allah ya jarrabe ni da shi, a kan abin da ya faru da dana, sannan kuma ko kadan ban ga laifin Maryam ba, amma a lokacin da aka yanke mata hukuncin kisa, addu’a na yi mata tare da rokon Allah ya ji kan ta da rahama, sannan na ce; idan aka kashe ta, wa zai kula da ‘ya’yanta guda biyu? Kawai za su girma ne a matsayin marayu, babu soyayyar uba, babu ta uwa,” in ji shi.

 

Da aka tambaye shi game da maganar da ‘yan’uwa suka yi na nuna damuwarsu kan afuwar da shugaban kasa ya yi mata sai ya ce; “Kowa yana da ‘yancin fadin albarkacin bakinsa a cikin iyalansa, amma a matsayina na mahaifinsa, na yafe mata.

 

Shi ma da yake yin nasa jawabin, Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya nuna matukar godiyarsa ga Alhaji Bello da sauran daukacin iyalansa, bisa irin halin da suka tsinci kansu a ciki; wanda ba kasafai suke nunawa ba.

 

Iyalan biyu, sun bayyana cewa, sun zabi afuwa, tausayi da kuma imani fiye da ciwon da yake damun su, sannan kuma sun himmatu wajen hada kai; domin renon yaran biyu, cikin kwanciyar hankali da soyayya.

 

Shi ma a nasa bangaren, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya zargi Shugaban Kasa Bola Tinubu, da yin amfani da ikon shugaban kasa na jin kai, ta hanyar yin afuwa ga mutum 175, yana mai cewa; matakin “ya gurgunta adalci”, sannan kuma yana da matukar hadari ga rashin bin doka da oda.

 

A cikin wata sanarwa da Atikun ya fitar, ta shafinsa na D a ranar Lahadin da ta gabata ya ce; hakkin yin afuwa, ba yana nufin rashin yin adalci ba ne ko tauye wa wani hakkinsa ba.

 

Har ila yau, Atiku ya soki shigar da mutanen da aka samu da aikata manyan laifuka, yana mai cewa; sakamakon wadanda aka yi wa afuwar, hakan na iya raunana imanin wasu daga cikin mutane tare da karfafawa wasu gwiwa, wajen ci gaba da aikata muggan laifuka.

 

Ya kara da cewa, bai kamata a bar yin afuwa ko jin kai ya hada su jera da aikata muggan laifuka da kuma rage aiwatar da adalci ba.

Tinubu
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda 'Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.