• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

- Ba Aure Ne Matsalar Kanawa Ba, Ƙarancin Ruwan Sha, Lantarki, Faɗace-faɗacen ‘Yan Daba Da Ƙwacen Waya - Farfesa Sheka

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano, karkashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf; ta shelanta ci gaba da gudanar da shirinta, na aurar da zawarawa da ‘yan mata wanda jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya kirkira; a zangon mulkinsa na farko.

A wancan lokaci, Sanata Kwankwaso ya aurar da zawarawa da ‘yan mata kimanin 1,000, inda shi ma bayan karbar mulkinsa a Jihar Kano, Injiniya Abba Kabiru Yusif; cikin ayyukansa na farko tun bayan rantsuwar kama aiki, shi ne auren zawarawa 1,800.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Duba da yadda Gwamnatin ke ganin shirin na da matukar alfanu, ya sa yanzu ma gabanin cikar Gwamnatin shekara guda a kan karagar mulkin Kano, aka fara shirye-shiryen sake aurar da wasu zawarawan, duk da cewa; a binciken da wakilinmu ya gudanar kan shirye-shiryen bikin auren zawarawan, Darakta Janar na Hukumar Gudanarwar Hukumar Hisba ta Jihar Kano, Alhaji Abba Sa’id Sufi ya shaida cewa, har yanzu ba a fitar da adadin wadanda za su amfana da shirin a wannan karo ba, wannan tasa har yanzu ba a iya gabatar da adadin kudaden da za a batar, domin aiwatar da shirin ba.

Sai dai kuma, bisa yanayin matsin tattalin arzikin da ake fama da shi ba ma a Kano ba kawai har ma da sauran sassan Nijeriya, ko ya dace gwamnati ta mayar da hankali a kan aurar da zawarawa duk da cewa akwai magidanta da yawa da ba su iya ciyar da iyalansu sannan akwai wasu matsaloli da suka addabi jihar fiye da na aure?

Farfesa Garba Ibrahim Sheka; na Jami’ar Bayero ta Kano, masani a fannin tattalin arziki; ya yi tsokaci a kan hakan, inda ya bayyana cewa; “a irin wannan lokaci, akwai bukatar yi wa wannan shiri kallon tsanaki, domin a tamu fahimtar; yanzu Kanawa ba aure suke bukata ba.

Labarai Masu Nasaba

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

“Akwai matsaloli da dama da suka fi aure bukatar a kai wa dauki, kamar misali matsalar karancin ruwan sha, hasken wutar lantarki, yawaitar fadace-fadacen ‘yan daba da kuma matsalolin kwacen waya, duk da cewa; mu Allah ya amintar da mu daga matsalar satar mutane da karbar kudaden fansa.”

Farfesa ya kara da cewa, a wasu lokutan batun auren zawarawa siyasa ce kawai, haka nan; wata hanya ce ta fitar da kudade, don amfani mahukuntan wajen biyan bikatun rayuwarsu. “Kazalika, babbar matsalar ma a nan ita ce, kamata ya yi a fara sama wa magidanta sana’o’in yi, wanda a hankalce ya fi zama masalaha kafin a zo batun aure.”

Sheka, ya ci gaba da cewa, a irin wannan hali idan aka yi wa wasu magidanta irin wannan aure, a karshe cikin shekara guda ko kasa da haka a fara samun matsalar daukar nauyin da ya kamata kowane maigidanci ya dauka, gazawar tasa kuma na iya jefa ma’auratan cikin tsaka mai wuya da hakan ka iya mayar da hannun agogo baya ta hanyar fadawa kowacce irin hanya, don kokarin rike gidan.

“Kamar yadda aka sani ne, al’adar Bahaushe ce; da zarar an yi Magana, sai wasu su fake da fadin cewa; Ma’aiki ya fadi cewa, ku yi aure ku hayayyafa; domin ya yi alfahari da yawanmu, to ya ilahi; yanzu Annabi (SAW), zai yi alfahari da yawan ‘yan daba da masu kwacen wayoyi ne? Don haka, abin da ya kamata shi ne; a yi la’akari da abin da al’umma suke bukata kafin kai wa ga yi musu wannan aure”, in ji Farfesa Sheka.

 Shi kuwa, wani magidanci Ibrahim Muhammad; wanda ya kwashe shekaru sama da 20 da yin aure, ya bayyana tasa matsayar; kan wannan batu na auren zawarawa, inda ya bayyana cewa; yanzu jama’a na neman yadda za a taimaka wa rayuwarsu ne kawai, ba maganar batun aure ba; musamman a irin wannan lokaci da cin abinci sau biyu ke neman gagarar mutane.

“Haka zalika, gagarumar matsalar karancin ruwan sha da wutar lantarki, suka fi zama wajibi gwamnati ta mayar da hankali a kansu, ta hanyar kashe wadannan makudan kudade, amma sai aka buge da batun auren zawararawa, don haka kamata ya yi a inganta rayuwar mutane; ta yadda kowa zai iya yi wa kansa wannan aure, ba tare da jiran gwamnati ko wani ba. Saboda haka, a nawa ganin wannan wata dabara ce ta wawashe kudaden talakawa kawai.” In ji shi.

 A nasa bangaren kuma, Tsohon Kwamandan Hukumar Hisba ta Kano, Sheikh Muhammad Ibn Sina, ya bayyana cewa, batun auren zawarawa abu ne da yake bukatar a yi wa kowane bangare kallon tsanaki.

“Da farko, hakkin gwamnati ne da zarar ta hangi yawaitar zinace-zinace a tsakanin al’umma, wadda ke sanadiyyar haifar da babban bala’i wanda kan iya shafar wanda ya aikata shi da kuma wanda bai ji ba, bai kuma gani ba. Saboda haka, idan aka tsinci kai a irin wannan hali; hakkin hukuma ne ta lalubo hanyoyin dakile yaduwar wannan musiba, wato yawaitar zina-zinace, ciki kuwa har da irin wannan yunkuri na aurar da zawarawa da ‘yan mata, musamman ganin su zawarawa sun taba yin aure sun san zakin da namiji.”

 Ibn Sina ya kara da cewa, a daya bangaren kuma; wajibi ne bayan an yi auren a nema wa ma’auratan hanyoyin da za a taimaka musu, domin dorewar auren, wanda ya hada da batun sama musu sana’o’in yi, don tafiyar da rayuwar yau da kullum, in ji shi.

Shi kuwa, wani matashi; dan gwagwarmaya mai suna Malam Rabi’u Basardaune, ya bayyana nasa ra’ayin ne da cewa; “yanzu ba aure ne a gaban matasa ba, babbar bukatarmu a halin yanzu ita ce; a sama mana da sana’o’in yi don dogaro da kawunanmu, sannan a dubi matsalar karancin ruwa da na wutar lantarki ga kuma uwa-uba matsalar fadace-fadacen ‘yan daba, wanda yake ci wa mutane tuwo a kwarya.

“Saboda haka, mu a halin yanzu ba ma goyon bayan wannan aure na zawarawa, a yi kokari a magance mana matsalar ruwan sha, sannan kuma ai shi wannan aure da ake yi; ai ba na kowa da kowa ba ne, na ‘yan Kwankwasiyya ne kadai, domin kuwa matukar kai ba dan Kwankwasiyya ba ne, kar ma ka yi zaton shiga cikin wannan tsari.” In ji shi.

Idan za a iya tunawa dai; lokacin da aka gudanar da auren zawarawa na karshe, Gwamnatin Jihar Kano; ta ware sama da Naira miliyan 800, domin yi wa zawarawa da ‘yan mata 2,000 aure, duk da cewa; a cikinsu 1,800 aka samu yi wa wannan hidima, sakamakon matsalolin da aka samu wajen gwajin lafiyarsu, inda aka samu wasu daga cikinsu dauke da wasu cututtuka; hakan ya sa aka dora wadanda aka samu da cututtukan a kan magani.

LEADERSHIP Hausa ta tuntubi mai neman zama Farfesa daga Jami’ar Tarayya ta Dutse, Ali Ado Siro; a kan ganin cewa an kashe Naira miliyan 800, wajen aurar da zawarawa na karshe ko bisa hasashe nawa za a iya kashewa a wannan karon wanda idan aka yi la’akari da yadda farashin Dala ya yi tashin gwauron zabi? Ya bayyana cewa za a iya kashe sama da Naira biliyan 4 da doriya.

Ya kara da cewa, a halin da ake ciki, da ake fama da matsalar ruwa a Kano, idan gwamnati za ta yi amfani da wadannan kudade, wajen inganta tare da gyara tashar ba da ruwan sha ta Tamburawa ko Chalawa, ko shakka babu jama’a za su fi yin farin ciki da hakan, ko kuma a yi amfani da su wajen kyautata wutar lantarki, wadda  jama’a ke ganin ita ta fi kyautuwa a gyara, kasancewar  da wutar lantarkin  ake yin amfani wajen tayar da injinan da ke samar da ruwan.

Yadda Ake Zaben Wadanda Za A Aurar

 Ganin cewa auren zawarawa shi ne aka yi hasashen irin sa na farko da aka taba aurar da mata 1000 a duniya a lokaci guda, wakilinmu ya duba hanyoyin da ake bi wajen zabo wadanda za a aurar a karkashin tsarin.

Auren wanda ake wa lakabi da ‘auren gata’, an samar da shi domin matan da suka rasa mazaje ta hanyar saki ko mutuwa da kuma ‘yan matan da suka isa aure amma halin matsin rayuwa ya hana su samun damar yin auren saboda wasu dalilai.

 Duk lokacin da gwamnati ke shirin gudanar da irin wannan aure ana amfani da kafofin yada labarai, majalisin jama’a, wuraren taruwar al’umma da makamanta ire-iren wadanann wurare ana sanar da masu bukatar shiga shirin da su garzaya shalkwatar hukumar Hisbah domin gabatar da kansu tare da karbar fam domin cikewa.

A farkon shirin, duk mai bukata yakan kai kansa hukumar Hisbah ne domin neman izinin shiga, amma daga baya ne aka fara shigar da siyasa, wanda ake raba damarmakin ga manyan ‘yan siyasa, jami’an gwamnati, shugabannin kananan hukumomi, a wani lokaci ma har da matan masu kwalli a ido.

 A baya an bayar da damar idan bazawari yana da bazawarar da yake so, za su iya kai kansu hukumar Hisba a yi bincike a tabbatar da sahihancin maganar tasu kafin amincewa da shigarsu tsarin, shi ma daga baya sai aka rika samun lauje cikin nadi, inda aka samu wani kwamandan Hisba na wata karamar hukuma saboda jin garabasar da auren ke da shi, matarsa ta aure ya kawo aka sake daura masu aure, kawai don su kwashi garabasa, wanda daga baya da hukumar ta smau wannan labari ta kwace kayan ta kuma dakatar da shi daga aiki.

 A lokacin da Sanata Kwankwaso ya kadammar da shirin na farko, an yi wa zawarawa da ‘yan mata 1,000 aure, sai kuma Gwamnatin Ganduje itama ta yi wa wani adadi da ya kai 500, yanzu kuma Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya yi wa zawarawa da ‘yan mata 1,800.

Ba a samu adadin yawan yaran da aka haifa ba a karkashin shirin auren, domin daga cikin wadanda suka samu shiga akwai wadanda suka fito daga kauyuka daban-daban da babu wata hanyar samun bayanin halin da suke ciki, sai da wasu dake da wayewa an hange su a lokacin bikin auren na wannan gwamnati sun kawo wa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso jikokinsa.

Wani matashi,Muhammad Kabir ya bayyana cewa, shi a cikin kabakin arzikin gwamnati da ke yawan tinkaho da shi bai ga abin da ya kai auren zawarawa amfani ba, domin a cewarsa, akwai uban wata bazawara da ta samu shiga wannan auren amma rashin kudin motar da zai kawo shi shalkwatar karamar hukumar ta sa bai zo ba, dole sai shugaban karamar hukumar ne ya zama waliyin yarinyar, “kenan idan aka ce sai wannan uban ya yi wa wannan yarinya kayan daki ba a san lokacin yin aurenta ba.” In ji shi

 Shi kuwa wani matashi da ya bukaci mu sakaya sunansa cewa ya yi, aure wani shiri ne kawai da aka tsara domin amfanin Kwankwasawa, “ni sau uku ina shiga cikin shirin amma saboda ba ni da wani dan Kwankwasiyya da ya tsaya min aka yi ta shakulatin bangaro da tawa bukatar.” A cewarsa.

 Babban abin da ake bukata a duk lokacin da aka tashi gudanar da shirin auren zawarawan shi ne gwaje-gwajen jini domin tantance lafiyar ma’auratn, kama daga gwajin cutar kanjamau, sikila da sauran cututtukan da suke da saukin dauka ta hanyar jima’i da cudanyar yau da kullum.

 Gwamnatin ke daukar nauyin duk wani abu da ake wa kowacce ‘ya, hakan ce ma tasa yanzu aka mayar da shirin auren zawarawan zuwa Auren ‘YAR GATA. Gwamnati na bai wa kowacce amarya sadaki, kayan daki, gyaran jiki, jari da sauran duk wani abu da ’yar gata iyayenta ke mata.

  • https://leadership.ng/tag/kano-mass-wedding/

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin YiAureAuren zawarawaGwamnatin KanokanoKarancin ruwan shaKwankwasiyyaKwankwasoRuwan Sha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yaushe Za A Kawo Karshen Karancin Man Fetur?

Next Post

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

Related

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

53 minutes ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

3 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

3 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

18 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

23 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

1 day ago
Next Post
Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya - Dakta Saleh

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.