ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

by Sani Anwar
2 years ago
Farashin

A yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa a kan rashin saukar farashin kayayyaki, Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Tabbatar da Zaman Lafiya da Wayar da Kai ta Kasa (NACOPEAM), Dakta Ahmad Saleh, ya bayyana hanyoyin da za a bi; don warware matsalar hauhuwar farashin kaya a Nijeriya.

Saleh ya bayyana abubuwan ne a shirin Barka Da Hantsi Nijeriya na Sashen Talabijin na Intanet na LEADERSHIP Hausa, da aka gabatar ranar Larabar da ta gabata.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo

Dakta Saleh, ya nunar da cewa matukar ana so a cimma burin haka, da farko ya kamata a kafa Hukumar Kayyade Farashi a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Idan ana so farashin kaya ya sauka a wannan kasa, wajibi ne a kafa wannan hukuma; wadda za ta yi aiki a lungu da sako na wannan kasa baki-daya.”

Kamar yadda Daktan ya bayyana a shirin, ya ce kafa wannan hukuma zai taimaka wajen kayyade farashin kayayyaki, inda ya bayar da misali da cewa ana sayar da Simintin Dangode a kan dubu shida da wani abu a Legas amma a Mambila Naira dubu tara ake sayarwa kuma a cikin kasa daya wanda haka bai kamata ba.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Haka zalika, dole ne wannan hukuma ta tabbatar da samar da farashin bai-daya a dukkanin kananan hukumomi 774 da muke da su a Nijeriya. “Wannan na daya daga cikin abubuwan da za su taimakawa wajen saukar farashin kayayyakin da ke ci wa ‘yan Nijeriya tiwo a kwarya a daidai wannan lokaci.” Ya bayyana.

Abu na biyu, kamar yadda Dr. Saleh ya bayyana shi ne, Bunkasa Masana’antun Cikin Gida: Bunkasa masana’antu zai taimaka kwarai da gaske wajen saukar farashin kayayyaki a cewar Masanin, domin kuwa a duk yayin da ya kasance abubuwan da ake shigowa da su; sun rinjayi wadanda ake fita da su, dole ne a fuskanci matsalar hauhawar farashin kaya.

Ya kara da cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen farfado da masana’antu tare da karfafa samar da abubuwan da za a rika fitar da su zuwa kasashen ketare, don sake farfado da tattalin arzikin wannan kasa, misali kamar bangaren harkar noma, ma’adanai da sauran makamantansu.

Domin kuwa, Nijeriya kasa ce da Allah ya azurta da dukkanin wani nau’i na arziki, wanda idan aka tsaya aka kyautata amfani da shi yadda ya kamata, za a samu kyautatuwar tattalin arziki da wadata da kuma jin dadi a kasar baki-daya.

Sai kuma na uku, da ya yi kiran a kafa Kotun Hukunta Duk Wanda Ya Bijire Wa Dokar Kasa: “Idan har ana so a cimma wannan manufa ta samun saukar farashin kayayyaki a fadin wannan kasa, ya zama wajibi ya kasance ana hukunta duk wanda ya ci karo da doka. Misali, a Kasar Ghana, lokacin da bankuna suka saba wa ka’idojin harkokin kudaden waje; ba tare da wani bata lokaci ba aka hukunta su”, in ji Daktan.

Don haka, ya zama dole Nijeriya ta mike tsaye wajen hukunta masu aikata laifuka, musamman ma wadanda aka samu da laifin cin hanci da rashawa, ya kasance ana yanke musu hukunci irin na babu sani; babu sabo. Dalili kuwa, babu abin da ya mayar da Nijeriya baya tare da dakile ci gabanta, kamar wannan dambarwa ta cin hanci da rashawa a wannan kasa, a cewar Dakta Sale.

Farashin
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.