ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

by Sani Anwar
2 years ago
Farashin

A yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa a kan rashin saukar farashin kayayyaki, Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Tabbatar da Zaman Lafiya da Wayar da Kai ta Kasa (NACOPEAM), Dakta Ahmad Saleh, ya bayyana hanyoyin da za a bi; don warware matsalar hauhuwar farashin kaya a Nijeriya.

Saleh ya bayyana abubuwan ne a shirin Barka Da Hantsi Nijeriya na Sashen Talabijin na Intanet na LEADERSHIP Hausa, da aka gabatar ranar Larabar da ta gabata.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo

Dakta Saleh, ya nunar da cewa matukar ana so a cimma burin haka, da farko ya kamata a kafa Hukumar Kayyade Farashi a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Idan ana so farashin kaya ya sauka a wannan kasa, wajibi ne a kafa wannan hukuma; wadda za ta yi aiki a lungu da sako na wannan kasa baki-daya.”

Kamar yadda Daktan ya bayyana a shirin, ya ce kafa wannan hukuma zai taimaka wajen kayyade farashin kayayyaki, inda ya bayar da misali da cewa ana sayar da Simintin Dangode a kan dubu shida da wani abu a Legas amma a Mambila Naira dubu tara ake sayarwa kuma a cikin kasa daya wanda haka bai kamata ba.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Haka zalika, dole ne wannan hukuma ta tabbatar da samar da farashin bai-daya a dukkanin kananan hukumomi 774 da muke da su a Nijeriya. “Wannan na daya daga cikin abubuwan da za su taimakawa wajen saukar farashin kayayyakin da ke ci wa ‘yan Nijeriya tiwo a kwarya a daidai wannan lokaci.” Ya bayyana.

Abu na biyu, kamar yadda Dr. Saleh ya bayyana shi ne, Bunkasa Masana’antun Cikin Gida: Bunkasa masana’antu zai taimaka kwarai da gaske wajen saukar farashin kayayyaki a cewar Masanin, domin kuwa a duk yayin da ya kasance abubuwan da ake shigowa da su; sun rinjayi wadanda ake fita da su, dole ne a fuskanci matsalar hauhawar farashin kaya.

Ya kara da cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen farfado da masana’antu tare da karfafa samar da abubuwan da za a rika fitar da su zuwa kasashen ketare, don sake farfado da tattalin arzikin wannan kasa, misali kamar bangaren harkar noma, ma’adanai da sauran makamantansu.

Domin kuwa, Nijeriya kasa ce da Allah ya azurta da dukkanin wani nau’i na arziki, wanda idan aka tsaya aka kyautata amfani da shi yadda ya kamata, za a samu kyautatuwar tattalin arziki da wadata da kuma jin dadi a kasar baki-daya.

Sai kuma na uku, da ya yi kiran a kafa Kotun Hukunta Duk Wanda Ya Bijire Wa Dokar Kasa: “Idan har ana so a cimma wannan manufa ta samun saukar farashin kayayyaki a fadin wannan kasa, ya zama wajibi ya kasance ana hukunta duk wanda ya ci karo da doka. Misali, a Kasar Ghana, lokacin da bankuna suka saba wa ka’idojin harkokin kudaden waje; ba tare da wani bata lokaci ba aka hukunta su”, in ji Daktan.

Don haka, ya zama dole Nijeriya ta mike tsaye wajen hukunta masu aikata laifuka, musamman ma wadanda aka samu da laifin cin hanci da rashawa, ya kasance ana yanke musu hukunci irin na babu sani; babu sabo. Dalili kuwa, babu abin da ya mayar da Nijeriya baya tare da dakile ci gabanta, kamar wannan dambarwa ta cin hanci da rashawa a wannan kasa, a cewar Dakta Sale.

Farashin
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.