• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Safarar Yaran Bauchi A Kano: Yadda Aka Sace Diyata ‘Yar Shekara 5 Daga Aiken Ta Shago –Malam Mukhtar

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Rahotonni
0
Safarar Yaran Bauchi A Kano: Yadda Aka Sace Diyata ‘Yar Shekara 5 Daga Aiken Ta Shago –Malam Mukhtar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

MUKHTAR SHUAIBU, mahaifin daya daga cikin yara bakwai da aka samu a Jihar Kano da ake zargin wasu sun sace daga Jihar Bauchi tare da kokarin sayar da su har da canza musu suna, ya bayyana irin tashin hankalin da suka shiga lokacin da ‘ya’yansu suka bace a tattaunawarsa da wakilinmu, KHALID IDRIS DOYA kamar haka:

Ka gabatar mana da kanka…
Sunana Muktar Shuaibu daga unguwar Federal Low Cost a cikin garin Bauchi.

Ta yaya satar yaran nan ta shafeka?
Kwarai da gaske lamarin ta shafeni. Daga cikin yaran, akwai wacce ake ce mata Asiya Mukhtar ‘yar shekara biyar ni ne mahaifinta. An sace ta ne ranar 8 ga watan Disambar 2023 da misalin karfe 10 na safiya.

Ya aka yi aka sace ta?
Hakan ya faru ne sakamakon an aike ta shago a kofar gidanmu a kan ta leka shagon ko an bude ko ba a bude ba ta zo ta fada wa mahaifiyarta. Fitar da ta yi ke da wuya, abun da bai wuce a yi cikin minti daya zuwa biyu ba, uwar ta ga ta wuce har minti biyar, sai ta fita ta leka ba ta gan ta ba. Nan take ta dawo ta dauki hijabi ta ce min ita fa ta aiki Ihsan amma ba ta ganta ba, bar ta je shagon ta duba. Ta je shagon ta duba aka ce mata yarinya dai ba ta zo shagon ba gaba daya.
Nan da nan bayan kamar mintina 30, sai na kai rahoto a ofis ‘yansanda da ke kusa da mu. Bayan nan, na je wajen masu unguwannin Federal Lowcost dukka na sanar musu halin da ake ciki tare da zuwa ofishin ‘yansanda na Dutsen Tanshi nan ma na kai rahoto aka dauki bayanaina. Suka ce min idan har zuwa yamma yarinya ba ta dawo ba na je na kai rahoto zuwa shalkwatan ‘yansanda, ban jira ma yammar ta yi ba na ja kai rahoton can.
Haka kuma na je gidajen rediyo dukka babu labari, duk inda ya dace dai mun kai rahoton bacewar ‘yarmu. Shiru kake ji, mu kuma hankalinmu na kara tashi.
Shiru-shiru dai sai muka samu labarin cewa an samu wani yaro a Kano kuma dan Bauchi ne, cewa an sace shi kuma an kama wacce ta sace shi a tashar mota a Mariri a lokacin da wata mata take kokarin tafiya da shi zuwa Legas. Kuma aka ce an samu labarin akwai wata mata da take sayar musu da yara daga Bauchi. Nan fa na tashi na kama bibiyar lamarin har na samu wanda ya kawo cikiyar yaron.
Da aka zo sai aka kama wacce take sayar mata da yaro daga Bauchi, muka ce tun da matar nan tana yankinmu ne domin Federal lowcost da Zango babu nisa duk yadda aka yi ta san wanda ya saci yarinyata, ko kuma inda yarinya take don haka muma za mu yi ta bibiya don mu samu karin haske.

Ita wannan matar da kuke zargi da cinikin yaran a Bauchi kun santa kuma mene ne sunanta?
Sunanta Ruth Yarima kuma yayanta ma gidansa na layinmu. Don haka mun santa, sannan mutanen unguwarmu da dama sun santa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Bayan da aka kamata ita Ruth daga Bauchi sai me ya faru?
Nan dai muka ji labarin cewa an samu wasu yara ‘yan Bauchi dukkansu da aka sace, amma za a ci gaba da bincike, in an ji labarin akwai yaranmu za a sanar da mu.
Cikin ikon Allah da aka je aka samu yaran, ‘yata ce ma a duk cikin sauran yaran ta iya bayanin sunanta na asali, ban da sunan da wadanda suka sace su suka sanya mata.

Kamar ya sunan da suka sanya mata?
Idan sun sace yara sai su canza musu suna da kuma addini tare da horar da su kafin su dauka su sayar a garuruwan Kudu. To ni ita yarinyata ba ta jima ba, domin ba ta wuce sati biyu ba a hannunsu, ba ta mance da wasu abubuwan ba. Ta iya fadin sunanta da muka sanya mata da sunana kuma ta ce ita ‘yar Bauchi ce. Aka tambaye ta a ina kike a Bauchi, sai da ta yi bayani har masallacin da ke kusa da kofar gidanmu ta kuma fadi sunan makarantar da take.
Daga cikin ‘yansandan da suka kamata na Kano ya ce ya yi aiki a Bauchi, akwai wanda ya sani a unguwarmu, bari ya tura masa hoton yarinyar a yi cigiya. Yana turo masa, sai mutumin ya bai wa limamin masallacin Juma’a na Federal Lowcost domin a yi cigiya, nan take a cikin masallacin wasu suka ce sun san ‘yata ce. Nan dai aka zo har masallacin kofar gidanmu aka neme ni tare da ba ni lambar wanda aka turo masa da hoton muka yi magana da shi.
An ce mu je Kano tare da hotuna guda biyu wanda aka dauka tare da yarinya da kuma shaidar takardar haihuwarta da mahaifiyarta domin a tabbatar da cewa ‘yarmu ce. Kafin ma mu tafi, sai aka sake turo hotonan wasu yaran Bauchi ana neman iyayensu.
An tura hotonan a ofishin ‘yansanda da ke Dutsen Tanshi, domin dukka iyayen da yaransu suka bata sun je sun kai rahoton hakan a wajen. Nan take DCO ‘yansanda da ke can ya kira iyayen da suka kawo rahoton domin su zo ko za su gane yaransu, Allah ya taima dukkanin yaran da aka turo an gane iyayensu.
Nan dai muka shirya muka tafi gaba dayanmu Kano a ranar Juma’a 22 ga watan Disamba, inda muka je shalkwatar ‘yansanda da ke Kano aka dauki bayananmu kuma aka tabbatar da cewa wadannan yaran ‘ya’yanmu ne.

Zuwa yanzu yaran suna hannunku?

Eh, Gwamnatin Bauchi ta mika mana ‘ya’yanmu bayan ta amso su daga hannun gwamnatin Kano.

Wani tashin hankali ka shiga lokacin da yarinka ta bace, kuma da aka same ta ya kuka ji?
Gaskiya mun yi matukar farin ciki lokacin da muka tabbatar an samu yarinyarmu, farin cikin ma ya wuce a misalta. A lokacin da aka sace yarinyar nan hankalina a tashe yake. Wallahi ni da mahaifiyarta ko barcin awa daya ba mu iya yi. Mun ga tashin hankali matuka, ko abinci ba ma iya ci yadda ya kamata.

Wani kira kuke da shi ga gwamnati?
Muna kira ga gwamnati da ta sanya ido, sannan muma iyaye mu kara kula. Sannan babban kiran da nake da shi ga gwamnati da hukumomin tsaro da sauran kungiyoyin da abun ya shafa da su tabbatar da sun yi tsayuwar daka har a hukunta wadanda aka samu da laifin satar yaranmu da sayar da su. A tabbatar an bincike su sosai domin gano kila ko suna da kungiya ko masu tallafa musu ko kuma wakilansu da har zuwa yanzu ba a kamasu ba, domin a tabbatar an zagolo sauran wadanda ba a kama ba zuwa yanzu.

…Gwamnan Kano Ya Jagoranci Sake Hada Yaran Da Aka Sato Daga Bauchi Da Iyayensu

Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir ya jagoranta sake hada yaran da aka sato daga Jihar Bauchi su 7 da iyayensu.
Hakan na kunashe cikin jawabin da daraktan yada labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya raba wa manema labarai a Kano.

Gwamnan ya jinjina wa kokarin rundunar ‘yansandan Jihar Kano karkashin jagorancin kwamishina, Muhammad Hussain Gumel. Ya bayyana matukar damuwarsa bisa yadda aka sato yaran tun daga Bauchi tare da yunkurin sayar da su a jihohin Anambara da Legas.
Kazalika, gwamnan ya bukaci iyayen yaran da su kara himma wajen kula da ‘ya’yansu, sannan ya yi kira ga takwarorinsa gwamnoni musamman gwamnan Bauchi da ya dauki matakin gaggawa domin damke wadanda ake zargin da aikia wannan mummunan lamari.

Rundunar ‘yansandar Jihar Kano ta samu nmasarar damke mutum 9 da ake zargi da aikata laifin a tashar motar Dake Mariri a lokacin da suke kokarin tserewa da yaran zuwa Jihar Legas.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan DamfaraJihar KanoSafarar kananan yara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bashin Amurka Ya Kai Sabon Matsayi Wanda Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasar

Next Post

Sin Ta Zamo Ta Daya A Yawan Rajistar Kamfanonin Sarrafa Farantan Samar Da Lantarki Ta Hasken Rana

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Sin Ta Zamo Ta Daya A Yawan Rajistar Kamfanonin Sarrafa Farantan Samar Da Lantarki Ta Hasken Rana

Sin Ta Zamo Ta Daya A Yawan Rajistar Kamfanonin Sarrafa Farantan Samar Da Lantarki Ta Hasken Rana

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.