• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sahihanci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sahihanci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kuna son cin Avacado? Kun san a nan kasar Sin ba a noma wannan nau’in ‘ya’yan marmari, saboda haka kusan ba wanda ya san shi kafin shekaru fiye da 10 da suka wuce.

Na tuna lokacin da na sayi Avacado a karon farko, ban san ya kamata a bari ya yi laushi ba kafin a ci shi. Sai na ci shi nan take bayan da na same shi, yayin da yake da tauri. Don haka ra’ayin da na samu game da Avacado a lokacin shi ne, wani nau’in ‘ya’yan marmari ne mai tsada, kuma maras dadi.

  • An Gudanar Da Dandalin Matasan Sin Da Afirka Kan Ayyukan Sa Kai

Tabbas daga bisani na san hanya mafi dacewa da ya kamata a bi wajen dandana Avacado. Kana saboda Sinawa sun kara fahimtar amfaninsa a fannin gina jiki, hakan ya sa ana shigo da karin Avacado cikin kasar Sin. Misali, a shekarar 2010, an shigo da Avacado ton 2 ne kacal cikin kasuwannin kasar Sin, amma zuwa shekarar 2018, wannan adadi ya karu zuwa ton 43,860, inda darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 133.

Ban da wannan kuma, tun daga shekarar bana, kasar Sin ta fara shigo da Avavado daga wasu kasasahen Afirka, irinsu Kenya da Tanzania.

Hakan na daga cikin matakan da aka dauka na cika alkawarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi a wani taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a bara, wato “Ba da sauki ga shigowar amfanin gonan Afirka cikin kasuwar kasar Sin, kana da kokarin shigo da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 30 daga kasashen Afirka, cikin shekaru 3 dake tafe.”
Me ya sa kasar Sin ke neman shigo da karin kayayyaki daga nahiyar Afirka? Dalili shi ne, kasar Sin na neman daidaita cinikayyar da ake yi tsakaninta da kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Bayanan da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta gabatar sun nuna cewa, ana samun daidaito tsakanin bangarorin Sin da Afirka ta fuskar ciniki.

Sai dai idan an tantance bayanai game da daidaikun kasa dake nahiyar Afirka, za a ga wasu kasashe na fitar da dimbin kayayyaki zuwa kasar Sin, yayin da wasu ba su samun damar fitar da kayayyakinsu sosai. Saboda haka, don raba moriya ga wadannan kasashe, kasar Sin ta dauki matakin shigo da karin kayayyakinsu.

Matakan da gwamnatin kasar Sin ta dauka a shekarun nan, sun hada da gudanar da tarukan baje kolin kayayyakin Afirka a kasar Sin, da kafa cibiyoyin nuna kayayyakin Afirka a wasu biranen kasar, da shirya bukukuwan tallace-tallacen kayayyakin Afirka a dandalin sayar da kaya ta kafar yanar gizo ta Internet, da samar da rance ga wasu kamfanonin kasar Sin domin su shigo da karin kayayyaki daga kasashen Afirka, da dai sauransu.

Kana sabbin matakan da kasar Sin ta dauka a bana, sun hada da fara shigo da Avacado daga kasashen Afirka, da yafe wa karin wasu kasashe mafi rashin karfin tattalin arziki harajin da ake karba bisa kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasar Sin, wadannan kasashe sun hada da Benin, da Burkina Faso, da Guinea Bissau, da Lesotho, da Malawi, da Sau Tome da Principe, da Tanzania, da Uganda, gami da Zambia.

Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin take da sahihanci, yayin da take hadin gwiwa tare da kasashen Afirka. Idan ana son kulla huldar hadin kai mai dorewa, dole ne a kulla huldar cin gajiyar juna. Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da hakan? Amsa ita ce ta yin mu’ammala cikin daidaito, da daidaita matakai akai akai, ta yadda za a iya tabbatar da daidaituwar moriyar bangarori daban daban, da sanya kowa ya gamsu.

Wannan ma dalili ne da ya sa kasashen Afirka, ba sa amincewa da wasu maganganu marasa kyau da wasu kasashe suka fada, game da huldar hadin gwiwar Afirka da Sin.

Kasashen Afirka sun ga sahihancin da kasar Sin ta nuna, kuma sun san duk wata matsalar da aka samu, yayin da ake hadin kai da kasar Sin, za a iya warware ta ta hanyar mu’ammala, da daidaita manufofi. Saboda haka, ba su damuwa game da huldar hadin kai da suka kulla tare da kasar ta Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Wasu Ma’aurata Kan Zargin Hada Baki Wajen Bizne Jaririyarsu Da Ranta A Jigawa

Next Post

2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

Related

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

52 minutes ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

2 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

2 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

5 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

5 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

7 hours ago
Next Post
2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

2023: Buhari Ya Hori Jami'an Tsaro Su Zama 'Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.