• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Yoyon Gurbatacciyar Ruwan Nukiliya Ta Fukushima Ya Aika Sako Ga Japan

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Fukushima

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Kamfanin wutar lantarki na Tokyo dake Japan ya sake gamuwa da wani lamari. Babban kamfanin samar da makamashin nukiliya mafi girma a kasar Japan, ya fada jiya cewa, mai yuwa kuskuren dan-Adam ne ya haddasa hadarin da ya faru da na’urar tsaftace gurbataccen ruwa a tashar makamashin nukiliya ta Fukushima Daiichi jiya. A lokacin, wani ma’aikaci ya gano cewa, ruwa na yoyo daga na’urar yayin da yake gogewa. Yana mai cewa, daga cikin bawuloli 16 da ya kamata a daure su da hannu yayin tsaftacewar, 10 a bude suke. Hakan ya sa ruwan dake dauke da sinadarin nukiliya, ya kwarara zuwa cikin bututun ya kuma haɗu da ruwan famfo.

A cewar rahotannin kafofin yada labaran kasar dake Fukushima, hadarin ya haifar da zubar a kalla tan 5.5 na gurbataccen ruwa. Kafofin yada labarai na cikin gida sun ba da rahoton cewa, matakin iska mai guba a wurin da lamarin ya faru, ya zarce sau 240 fiye da na yankin da ke kewaye.

  • An Gama Aikin Bitar Liyafar Bikin Bazara Karo Na 5 Ta Kasar Sin
  • Shugaban Miyetti Allah, Abdullahi Bodejo Mutum Ne Mai Yi Wa Nijeriya Fatan Alhairi

Al’ummar duniyar ba ta yi mamakin sake afkuwar wani hadari a TEPCO ba. Tun bayan hatsarin tashar makamashin nukiliya ta Fukushima a shekarar 2011, wannan kamfani ya fuskanci hadurra da badakala iri-iri daga lokaci zuwa lokaci. Amma ko shi kansa kamfanin, ba zai iya bayyana jimillar adadin ba.

Tun daga watan Agustan shekarar da ta gabata, Japan ta zubar da gurbatccen ruwan nukiliya har sau uku a cikin tekun, inda ta zubar da ruwan dagwalon nukiliya da ya kai sama da tan dubu 23. A wannan watan ne kuma, ake sa ran za a fara zagaye na hudu na zubar da ruwan dagwalon a cikin teku. Wani sabon hadarin da ya afku a TEPCO, ya sake ankarar da bangaren Japan. Don haka, ya kamata ’yan siyasar Japan su dauki alhakin lamarin, da yin taka tsan-tsan wajen tunkarar hadurran tsaron kamfanin TEPCO, da yin kira da a dakatar da tsare-tsaren fitar da hayaki mai guba nan gaba, da yin shawarwari da kasashen duniya, da samar da mafita da dukkan bangarori suka amince da shi. (Mai Fassarawa: Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

George Ga Atiku: Ka Bari Matasa Masu Jini A Jika Su Yi Takara A 2027

Next Post

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Ba Za Mu Taba Cin Amanar ‘Yan Nijeriya Ba -Majalisa

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

10 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

12 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

12 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

14 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

14 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

16 hours ago
Next Post
majalisar kasa

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Ba Za Mu Taba Cin Amanar ‘Yan Nijeriya Ba -Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.