ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Ba Za Mu Taba Cin Amanar ‘Yan Nijeriya Ba -Majalisa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
majalisar kasa

Majalisar wakilan Nijeriya ta bayyana cewa tana da kwarin giwa kan mataimakin shugaban majalisa, Rt. Hon. Benjamin Kalu, zai sauke nauyin da aka dora masa na shugabancin kwamitin gyaran kundin tsarin mulki, wanda ba za su taba cin amanan ‘yan Nijeriya ba.  

A kwanan nan ne majalisar ta kafa kwamiti da zai duba shawarwari na canje-canje da gyare-gyare na kundin tsarin mulki na shekarar 1999, inda aka dora shugabancin kwamitin ga Kalu tare da wasu kwararrun ‘yan majalisa a matsayin mambobi.

  • Ku Je Ku Magance Matsalar Yunwa Da Ta Addabi Jama’a -Fintiri
  • Babu Inda Na Ce Na Fi ‘Yan Nijeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa -Ɗangote

Wannan kwamiti shi ne na shida da aka kafa tun a shekarar 1999, domin sake duba kundin tsarin mulki da ake amfani da shi a yanzu, ana tsammanin za a kaddamar da shi a ranar 26 ga Fabrairun 2024.

ADVERTISEMENT

Da yake yi wa ‘yan jarida karin haske a Jihar Kano, mai magana da yawun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Philip Agbese ya bayyana cewa ‘yan majalisa suna da kwarin gwiwa a kan mataimakin shugaban majalisar wakilai, kuwa kwamitinsa zai yi aikin da aka dora masa kan lokaci.

Ya ce, “Tun lokaci mai tsawo majalisar kasa take yunkurin sake fasalin kundin tsarin mulki na shekarar 1999, tare da niyyar sauya wasu daga cikin dokokin ta yadda za su dace da zamani. A wasu lokutan, majalisa na samun nasara, amma kuma a wani sa’ilin kwamitin majalisa yakan gaza yin aikinsa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Amma wannan kwamitin da aka danka wa Rt. Hon. Benjamin Kalu zai samu nasarar yin aikin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan. Ya kamata ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalinsu a rana daya komai zai iya sauyawa.

“Wannan kwamitin zai yi amfani da shawarwarin mutane da mabambantan masu ruwa da tsaki da kungiyoyin fararen hula da ma’aikatun gwamnati da masarautun gargajiya da kungiyoyin mata da kuma ‘yan kasuwa masu zaman kansu wadanda suke taimakawa wajen bunkasa tattalin arziki, domin samun nasarar gyarar kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

Haka kuma Hon. Agbese ya bayyana cewa wannan lokaci ne da kungiyoyi da ma’aikatun gwamnati za su samu dama na sauya wasu daga cikin dokokin tsarin mulki na 1999, domin yin aiki kafada da kafada da wakilansu a lokacin da kwamitin ya fara aiki a hukumanci a kasrshen wannan wata.

“Akwai kudurorin doka guda 40 da majalisa ke neman a saka su a cikin tsarin mulki. Wasu daga ciki za su kawo karshen matsalolin jinsi da masarautun gargajiya da bai wa kananan hukumomin ‘yancin gashin kai da matsalolin kudade da dai sauransu.

“Kwamitin zai tabbatar ya kammala aikinsa a watan Disambar 2025. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da su yi aiki kafada da kafada da wakilolinsu da kwamitin saboda a kammala aikin kan lokaci.”

Mataimakin shugaban majalisar wakilai kuma shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulki ya gana da dukkan mambobin kwamitin a ranar Laraba da ta gabata, inda ya yi alkawarin cewa kwamitin zai kammala aikinsa a watan Disambar 2025.

Kalu ya bukaci mambobin kwamitin da su shirya yin aiki tukuru saboda samun damar yi sauye-sauye na kundin tsarin mulki kan lokaci kamar yadda suka yi wa ‘yan Nijeriya alkawari.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Majalisa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
bikin bazara

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.