ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Ba Za Mu Taba Cin Amanar ‘Yan Nijeriya Ba -Majalisa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
majalisar kasa

Majalisar wakilan Nijeriya ta bayyana cewa tana da kwarin giwa kan mataimakin shugaban majalisa, Rt. Hon. Benjamin Kalu, zai sauke nauyin da aka dora masa na shugabancin kwamitin gyaran kundin tsarin mulki, wanda ba za su taba cin amanan ‘yan Nijeriya ba.  

A kwanan nan ne majalisar ta kafa kwamiti da zai duba shawarwari na canje-canje da gyare-gyare na kundin tsarin mulki na shekarar 1999, inda aka dora shugabancin kwamitin ga Kalu tare da wasu kwararrun ‘yan majalisa a matsayin mambobi.

  • Ku Je Ku Magance Matsalar Yunwa Da Ta Addabi Jama’a -Fintiri
  • Babu Inda Na Ce Na Fi ‘Yan Nijeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa -Ɗangote

Wannan kwamiti shi ne na shida da aka kafa tun a shekarar 1999, domin sake duba kundin tsarin mulki da ake amfani da shi a yanzu, ana tsammanin za a kaddamar da shi a ranar 26 ga Fabrairun 2024.

ADVERTISEMENT

Da yake yi wa ‘yan jarida karin haske a Jihar Kano, mai magana da yawun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Philip Agbese ya bayyana cewa ‘yan majalisa suna da kwarin gwiwa a kan mataimakin shugaban majalisar wakilai, kuwa kwamitinsa zai yi aikin da aka dora masa kan lokaci.

Ya ce, “Tun lokaci mai tsawo majalisar kasa take yunkurin sake fasalin kundin tsarin mulki na shekarar 1999, tare da niyyar sauya wasu daga cikin dokokin ta yadda za su dace da zamani. A wasu lokutan, majalisa na samun nasara, amma kuma a wani sa’ilin kwamitin majalisa yakan gaza yin aikinsa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Amma wannan kwamitin da aka danka wa Rt. Hon. Benjamin Kalu zai samu nasarar yin aikin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan. Ya kamata ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalinsu a rana daya komai zai iya sauyawa.

“Wannan kwamitin zai yi amfani da shawarwarin mutane da mabambantan masu ruwa da tsaki da kungiyoyin fararen hula da ma’aikatun gwamnati da masarautun gargajiya da kungiyoyin mata da kuma ‘yan kasuwa masu zaman kansu wadanda suke taimakawa wajen bunkasa tattalin arziki, domin samun nasarar gyarar kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

Haka kuma Hon. Agbese ya bayyana cewa wannan lokaci ne da kungiyoyi da ma’aikatun gwamnati za su samu dama na sauya wasu daga cikin dokokin tsarin mulki na 1999, domin yin aiki kafada da kafada da wakilansu a lokacin da kwamitin ya fara aiki a hukumanci a kasrshen wannan wata.

“Akwai kudurorin doka guda 40 da majalisa ke neman a saka su a cikin tsarin mulki. Wasu daga ciki za su kawo karshen matsalolin jinsi da masarautun gargajiya da bai wa kananan hukumomin ‘yancin gashin kai da matsalolin kudade da dai sauransu.

“Kwamitin zai tabbatar ya kammala aikinsa a watan Disambar 2025. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da su yi aiki kafada da kafada da wakilolinsu da kwamitin saboda a kammala aikin kan lokaci.”

Mataimakin shugaban majalisar wakilai kuma shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulki ya gana da dukkan mambobin kwamitin a ranar Laraba da ta gabata, inda ya yi alkawarin cewa kwamitin zai kammala aikinsa a watan Disambar 2025.

Kalu ya bukaci mambobin kwamitin da su shirya yin aiki tukuru saboda samun damar yi sauye-sauye na kundin tsarin mulki kan lokaci kamar yadda suka yi wa ‘yan Nijeriya alkawari.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
bikin bazara

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.