• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sakin-mara Ga Masu Sanya-ido A Zabe

by Muktar Anwar and Sulaiman
7 months ago
in Bakon Marubuci
0
inec
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga cikin dalilan da suka kara bai wa wannan hadakar kungiyoyi tamu ta masu kishin jihar Kano kwarin-gwiwar sanya na-mujiya cikin sha’anin wannan zabe na kananan hukumomi da hukumar zaben ta Kano (KANSIEC) ta gudanar, karkashin jagorancin Farfesa Sani Lawan Malumfashi, bai wuce yin maraba tare da sahalewa kungiyoyin al’umma shigowa cikin sabgar ka’in da na’in da hukumar zaben ta yi ba. A daya hannun, ta tabbata cewa, ita ma gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin maigirma Abba Kabir Yusuf, ba tai yunkurin farmakar masu sanya-idanu cikin sha’anin zabukan ba.

 

Batun sahalewa kungiyoyin al’umma na gida da na waje, sanya-idanu cikin sha’anin zabukan wannan kasa, wani al’amari ne mai wuyar sha’ani, musamman ga gwamnatocin da babban burinsu shi ne, su sami nasarar lashe zabuka ta kowane hali. Ba ya ga irin wadannan gwamnatoci, hukumomin zabe ma da aka nada su, kan marawa shugabannin gwamnati baya, wajen kange kungiyoyin al’umma, ga barin sanin irin wainar da ake toyawa cikin harkokin zabukan, a cikin sako da lungu na kasar.

  • Okawa Bai Taimake Ni Da KuÉ—in Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku
  • Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti

Cikin zabukan Shekarar 2007, kungiyar kare hakkin dan’adam “Human Rights Watch” ta yi taro da “yan jaridu, tare da raba musu takardar bayan taro, mai taken “Election or Selection” (Zabe ko Nadi). Bugu da kari, kungiyar, ta yi kalubale ga hukumar zabe da kuma gwamnatin tarayya, tana mai zarginsu da hadin-baki tare da jan-kafa da hukumar zaben ke yi, na kin tantance kungiyoyin sanya-ido a zabe bisa lokaci, kamar yadda dokokin zaben suka lamunce.

 

Labarai Masu Nasaba

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

(Daily Trust, April 5, 2007).

Har ila yau, ba ya ga gwamnatoci da hukumomin zabe, ta tabbata hatta jami’an tsaro ma na da mugun tabo, wajen nuna kyama da kuma kyarar irin wadannan kungiyoyi namu na al’umma da ke bin-diddigin batutuwan zabukan a Kasa. Cikin zabukan Shekarar 2007, an gabatar da wasu kunshin rahotannin da ke hakkake cewa, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), sun ta kai farmaki a kan kungiyoyin sanya-idanu a zabukan Shekarar. Jami’an tsaron, na kafa hujjar cewa, wai jam’iyyun “yan adawa ne ke daukar nauyin kungiyoyin.

 

(Daily Trust, April 3, 2007).

A karshe, wannan hadakar kungiyoyin al’uma namu da ke rajin kishin wannan jiha tamu ta Kano, na matukar yaba irin yadda shugaban hukumar zabe ta Kano, Farfesa Sani Lawan Malumfashi, ya zage dantse tare da jajircewa, wajen gudanar da zabukan kananan hukumomi a jihar, duk da irin bita da kulli da ya rika fuskanta dare da rana. Ya ba da lokacinsa da ma ransa, wajen ganin ya ba da gudunmuwar samawa kananan hukumomin na Kano shugabanci nagari, wadanda jama’ar gari ke zabarsu, don gudanar musu da ayyukan da za su taba rayuwarsu tabawa.

Wadannan nasarori da shugaban hukumar zaben ya tsuwurwurta, ba su kasance nasa ne shi kadai ba, haka ba na gwamnatin Kano ba ne ita kadai. Gaskiyar magana, irin wadannan gwala-gwalan nasarori da ya girba, sun zamto ne na daukacin jama’ar jihar Kano ne baki daya. Domin kuwa, da wannan zabe ya zo da tangardar da za ta jaza salwantar rayuka da dukiyoyi, da ba wannan zance ne ake yi ba yanzu. Da mai yi wa, hatta wannan tsokaci namu ba zai rubutu ba.

Babu shakka, zai yi matukar ma’ana, ya zamana sauran hukumomin zabe da za su zo nan gaba, su zamto suna masu yin koyi ne da irin salon malaminmu Farfesa Sani Lawan Malumfashi, wajen jajurcewa tare da gudanar da ingantattun zabuka, don nasarar Jihar Kano, da ma Nijeriya bakidaya.

 

Kawowa Zaben Kano Tarnaki Tamkar Rashin Kishin-kai Ne

Sanin kowa ne a Kano cewa, wasu mutane sun yi yunkurin hana gudanar da zabukan kananan hukumomi da hukumar zabe ta Kano ta tasamma yi, inda suka garzaya zuwa Kotu, tare da karbo umarnin Kotu, na dakatar da duka zabukan bakidaya. Ko ma mene ne dalilin masu karar, ba shi ne abin kallo ba, a gabar da ake ciki. Kamar yaya?. Abin la’akarin shi ne, gwamnatin tarayya hada da kotun koli ta kasa, sun ci alwashin kin yarda a bai wa kowace karamar hukuma kudin wata-wata da ake ba su daga asusun tarayya, muddin ba a gudanar da zabukan kananan hukumomi a cikin Watan na Oktobar (October, 2024), da ake ta dambarwar zuwa Kotunan Shari’a a cikinsa ba, cewa, a yi zaben, koko ka da ma a yi.

 

Akwai masu ra’ayin cewa, yunkurin dakatar da jihar Kano aiwatar da zabukan, tamkar wani tarko ne da aka so yi wa jihar ta Kano, don ta yi adabo da wadancan kudaden na kananan hukumomi. Ba sai an yi wa mai karatu wani dogon bayani ba, rashin ci gaba da shigowar wadancan kudade, zai iya kassara rayuwar miliyoyin jama’ar Kano ta mabanbantan fuskoki. Sai wasu suka yi tsai, tare da yin jinjina ga tutsun da gwamnatin Kano da hukumar zaben suka yi, na cewa, babu makawa sai sun gudanar da zabukan, duk da cewa, ba kowa ne ya fahimci fa’idar kafiyar da suka nuna ba.

 

Bangaren Shari’a Kan Yi Wa Dimukradiyya Lahani

Duk da irin tsantsar muhimmancin da tsagin shari’a ke da shi karkashin tsarin dimukrradiyya, an wayigari a wannan Kasa, inda dubban mutane ke munana masa zato. Babu yadda za a yi, aji-dadin gudanar da ita kanta dimukrradiyyar, muddin za a bar jama’a su ci gaba da rayuwa sasakai, ba tare da wasu dokoki na yi musu iyaka da kuma linzami ba. Sai dai, akwai masu kokarin faiyace irin mugunyar rawar da ake zargin bangaren shari’ar Kasar ke takawa, cikin lamuran siyasar Kasar, musamman cikin wannan zubin jamhuriyar siyasa ta hudu da muke ciki. Sai aka wayigari, tamkar tsagin masu mulki ne suka fi sauran jama’ar gari amfanuwa daga bangaren na shari’a a Kasar.

 

Dambarwar Babban Maishari’a Katsina-alu da Shugaba Salami, 2007

Da yawan masharhanta na da tunanin cewa, zanin bangaren shari’a a Najeriya bai taba sillewa karara ba a bainar jama’a, tare da yi mata tonon sililin takan kaucewa gaskiya, cikin batutuwan siyasar wannan Kasa, irin yadda ya faru cikin Shekarar zaben 2007, tsakanin babban maishari’a na Kasa Katsina-alu, da maishari’a kuma shugaban sashen kotunan daukaka kara na Kasa, Salami, game da batun kujerar gwamnan Sokoto. Ko ba a yi wa mai karatu dalla-dalla ba, zai fahimci akwai mai son yin awon-gaba da kujerar gwamnan cikinsu, gudan kuma, na son tabbatar da ita ne (wannan haka yake).

 

(Source, February 21, 2011: 5, 30, 33, 3b).

Babban dalilin kawo wancan misali dake sama shi ne, akwai wadanda mamaki ya karsu cewa, ta yaya ne za a ce Kotun Koli ta yi wa’adin wajibcin gudanar da zabukan kananan hukumomin lallai cikin Watan na Oktobar 2024, amma wasu “yan siyasa, su je, su amso wata takarda daga wata kotun da ba ta kai ta koli daraja ba, wadda za ta haramta gudanar da zaben a cikin wannan Wata da ta iyakance gudanar da zabe cikinsa!

Koma mene ne mafitar gwamnatin jihar Kano da kuma hukumar zaben ta jihar, da yawan mutane na da tunanin cewa, gudanar da zabukan ne mafi a’ala sama da kin aiwatar da su. Bugu da kari, kaurin-suna da manyan kotuna da manyan alkalai suka yi a Kasar, cikin batutuwan siyasa, na daga dalilan dake sanyawa a gaza fahimtar kotunan, ko da kuwa hukuncin da suka furzar akan hanya yake.

 

Shari’ar Nasiru Yusuf Gawuna Da Dahiru Abdu Oska, 2007

Irin yadda batun shari’ar tsohon mataimakin tsohon gwamnan Kano, Nasiru Gawuna ta gudana, tsakaninsa da abokin bugawarsa, wato Dahiru Oska, ita ma ta bar gagarumin miki tsakanin alkalan da kuma jama’ar Kano, game da batun sabgar siyasa.

An yi waccan shari’a ne bayan kammala babban zabe na Kasa na Shekarar 2007, inda Gawuna ke yin takarar kujerar shugaban karamar hukumar Nassarawa karkashin jam’iyyar ANPP, shi kuma Oska ke yin tasa takarar ta kujerar shugabancin karamar hukumar ta Nassarawa a karkashin jam’iyyar PDP. Bayan hukumar zabe ta aiyana Gawuna a matsayin wanda ya sami nasarar lashe zaben, sai Oska ya shigar da kara kotu. Wani abin ban mamaki, sai da lokacin saukar Gawuna daga kan kujerar shugabancin karamar hukumar ya yi, sannan ne aka yanke hukunci. Sai Alkali ya tabbatar da nasarar lashe zaben ga Abdu Oska. Sai dai, ko daga garin gaba-gaba mutum ya fito, ba shi iya ba da kyakkyawar fassara ga wannan hukunci, wanda sai bayan Shekara uku ne aka iya gano cewa, Nasiru Yusuf Gawuna haramtacciyar kujerar mulki ce ya hau, wanda ba hakkinsa ba ne.

Lokaci ya yi da ya kamata bangaren na shari’a da ya tsaya ya yi karatun ta-natsu, wajen kare mutuncin kansa, da yin amai ko ruwan hukunce-hukunce bisa doron gaskiya, tare da kaucewa duk wasu burace-burace na siyasa, da za su ci gaba da afkar da munanan zato a tsakanin jama’ar gari da kotunan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Okawa Bai Taimake Ni Da KuÉ—in Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Next Post

An Yaye Dalibai 15,139 Masu Digirin NCE A Adamawa

Related

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

2 days ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

2 weeks ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

2 months ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]

2 months ago
Next Post
An Yaye Dalibai 15,139 Masu Digirin NCE A Adamawa

An Yaye Dalibai 15,139 Masu Digirin NCE A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.