• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salmai Albasu: Mawakiyar Da Ta Rera Wakar Soriye Ta Cika Shekara 70

by Rabilu Sanusi Bena
9 months ago
Salmai

Mun gode wa gwamnatin tarayya ‘yan’uwa

Ta raba mu da kwakudubar bana

Ta kawo Geron taimako, ta kawo dawar taimako,

Arayye ga Garin Kuli-kuli ga Garin Kwaki,

Arayye an yi rabo na gaskiya ba a cuci kowa ba,

LABARAI MASU NASABA

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Ga Angurya ga Budu ta ce a bai wa dabobi,

Kusan ta gyaro Lautai,

Arayye don ga Laturu da Famfo ma an kawo,

Arayye saura Rediyo Girim mai wakar Soriye”.

Wadansu baitoci kenan a cikin wakar Soriye, wadda tsohuwar mawakiya Salmai Albasu ta rera, domin jinjina wa gwamnatin waccan lokaci; kan yadda ta kawo abubuwan more rayuwa da abinci ga takalawa, wannan waka ta yi matukar tasiri a shekarun baya, sannan har yanzu wasu gidajen rediyon kan saka ta a zabukansu; lokaci bayan lokaci.

“Shekara kwana ga mai tsawon rai”, in ji Bahaushe. Haka kuwa maganar take, domin kuwa matashiyar da ta rera dadaddiyar wakar; mai dadin sauraro a shekarun baya, mai taken Soriye, wadda kuma ta yi tasiri a kunnuwan masu sauraren wakokin Hausa, musamman a gidajen rediyo a wancan lokaci; yau ta cika shekara 70 cif a raye.

Salmai Albasu, ba sabon suna ba ne a wajen mutane masu sha’awar sauraran rediyo, musamman masu amfani da harshen Hausa, yau an wayi gari ta daina wakar amma har yanzu a kan saka wakokinta shahararru a gidajen rediyon da ke Arewacin Nijeriya.

Salmai, a wata hira da ta yi da BBC Hausa ta bayyana cewa; ita haifaffiyar Albasu ce da ke Jihar Kano, dukkanin iyayenta Katsinawa ne, amma kuma mazauna garin Albaus, ta bayyana cewa; tun a lokacin da ‘yan mata ke yin rawar dandali yayin da makada ke kida ta fara yin waka, inda a wancan lokacin take yin waka, wadansu ‘yan mata kuma ke yi mata amshi.

“Daga wasan kuruciya na ‘yan mata na fara waka, a wancan lokaci; akwai makada da dama da ke kida, ni kuma da sauran kawayena muna waka, amma ni ce nake rera wakar; su kuma suna yin amshi har ta kai ga na ci gaba da yin wakoki. Sannan, ana daukar mu zuwa Sakatariyar Karamar Hukuma, muna wayar da kan al’umma a wancan lokaci, saboda a wancan lokaci; mutane ba su waye da harkar karatun boko da sauran shirye shiryen gwamnati ba.

Wannan dalili ne yasa ake zuwa da mu gari-gari, muna yin waka mutane na jin dadi suna yi mana likin kudi muna kwasa. Haka nan, babu abin da za mu cewa waka, sai san barka; domin kuwa saboda ita na ziyarci wurare da dama a Arewacin Nijeriya, har ma da Kudanci, misali kamar Jihar Legas.

Har ila yau, dangane da makada da sauran abokan aikin Salmai a wancan lokaci, Dattijuwar ta ce akwai Sarkin makada Sule, Tunare, Shu’aibu Kwata, wanda yake maroki ne, sai kuma bangaren masu yi mata amshi akwai; Subdi da Uwani wadanda dukkansu Allah ya yi musu rasuwa.

Wakoki kamar Soriye, A kai yara makaranta, Ku san ilimi mu ji dadi da sauransu, su ne wakokin da suka fi shahara a cikin wakokin da zabiyar ta yi. Kazalika, Salmai ta bayyana cewa; a lokacin da take kan ganiyarta, ta fi mayar da hankali wajen wakokin da suka shafi cin zarafin ‘ya’ya mata da kuma na zaburar da mutane, musamman yara kanana da su nemi ilimin addini da na book, ganin yadda a wancan lokacin ake tsanar ilimin boko a Arewacin Nijeriya.

Dangane da batun ko ta samu wani a cikin ‘ya’yanta da ya gaje ta a wannan sana’a ta waka? Sai Salmai ta ce, ko kusa babu wani daga cikin yaranta su bakwai da ta haifa da ya nuna sha’awar harkar waka, hasali ma mafi yawancinsu tuni sun yi aure; sun tare a gidajen mazajensu, amma dai a cewar tata; har yanzu idan aka kunna wakokinta a gidajen rediyo, hakan na matukar saka ta farin ciki tare da tuna mata shekarun kuruciyarta.

A zamanin baya, gwamnatoci sun yi amfani da wakoki da sauran hanyoyi wajen wayar da kan mutane, musamman wadanda ke zaune a karkara, domin nusar da su muhimmancin neman ilimin addini da na boko, tsabtace wajen muhallinsu da kuma hanyoyin da za su bi wajen kare kansu daga wasu cututtuka daban-daban a wancan lokaci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Next Post
Mutane Da Dama Sun Jikkata Yayin Da Tanka Ta Yi Bindiga A Abuja

Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Bindigar Tankar Mai A Enugu

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.