ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salmai Albasu: Mawakiyar Da Ta Rera Wakar Soriye Ta Cika Shekara 70

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Salmai

Mun gode wa gwamnatin tarayya ‘yan’uwa

Ta raba mu da kwakudubar bana

Ta kawo Geron taimako, ta kawo dawar taimako,

ADVERTISEMENT

Arayye ga Garin Kuli-kuli ga Garin Kwaki,

Arayye an yi rabo na gaskiya ba a cuci kowa ba,

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Ga Angurya ga Budu ta ce a bai wa dabobi,

Kusan ta gyaro Lautai,

Arayye don ga Laturu da Famfo ma an kawo,

Arayye saura Rediyo Girim mai wakar Soriye”.

Wadansu baitoci kenan a cikin wakar Soriye, wadda tsohuwar mawakiya Salmai Albasu ta rera, domin jinjina wa gwamnatin waccan lokaci; kan yadda ta kawo abubuwan more rayuwa da abinci ga takalawa, wannan waka ta yi matukar tasiri a shekarun baya, sannan har yanzu wasu gidajen rediyon kan saka ta a zabukansu; lokaci bayan lokaci.

“Shekara kwana ga mai tsawon rai”, in ji Bahaushe. Haka kuwa maganar take, domin kuwa matashiyar da ta rera dadaddiyar wakar; mai dadin sauraro a shekarun baya, mai taken Soriye, wadda kuma ta yi tasiri a kunnuwan masu sauraren wakokin Hausa, musamman a gidajen rediyo a wancan lokaci; yau ta cika shekara 70 cif a raye.

Salmai Albasu, ba sabon suna ba ne a wajen mutane masu sha’awar sauraran rediyo, musamman masu amfani da harshen Hausa, yau an wayi gari ta daina wakar amma har yanzu a kan saka wakokinta shahararru a gidajen rediyon da ke Arewacin Nijeriya.

Salmai, a wata hira da ta yi da BBC Hausa ta bayyana cewa; ita haifaffiyar Albasu ce da ke Jihar Kano, dukkanin iyayenta Katsinawa ne, amma kuma mazauna garin Albaus, ta bayyana cewa; tun a lokacin da ‘yan mata ke yin rawar dandali yayin da makada ke kida ta fara yin waka, inda a wancan lokacin take yin waka, wadansu ‘yan mata kuma ke yi mata amshi.

“Daga wasan kuruciya na ‘yan mata na fara waka, a wancan lokaci; akwai makada da dama da ke kida, ni kuma da sauran kawayena muna waka, amma ni ce nake rera wakar; su kuma suna yin amshi har ta kai ga na ci gaba da yin wakoki. Sannan, ana daukar mu zuwa Sakatariyar Karamar Hukuma, muna wayar da kan al’umma a wancan lokaci, saboda a wancan lokaci; mutane ba su waye da harkar karatun boko da sauran shirye shiryen gwamnati ba.

Wannan dalili ne yasa ake zuwa da mu gari-gari, muna yin waka mutane na jin dadi suna yi mana likin kudi muna kwasa. Haka nan, babu abin da za mu cewa waka, sai san barka; domin kuwa saboda ita na ziyarci wurare da dama a Arewacin Nijeriya, har ma da Kudanci, misali kamar Jihar Legas.

Har ila yau, dangane da makada da sauran abokan aikin Salmai a wancan lokaci, Dattijuwar ta ce akwai Sarkin makada Sule, Tunare, Shu’aibu Kwata, wanda yake maroki ne, sai kuma bangaren masu yi mata amshi akwai; Subdi da Uwani wadanda dukkansu Allah ya yi musu rasuwa.

Wakoki kamar Soriye, A kai yara makaranta, Ku san ilimi mu ji dadi da sauransu, su ne wakokin da suka fi shahara a cikin wakokin da zabiyar ta yi. Kazalika, Salmai ta bayyana cewa; a lokacin da take kan ganiyarta, ta fi mayar da hankali wajen wakokin da suka shafi cin zarafin ‘ya’ya mata da kuma na zaburar da mutane, musamman yara kanana da su nemi ilimin addini da na book, ganin yadda a wancan lokacin ake tsanar ilimin boko a Arewacin Nijeriya.

Dangane da batun ko ta samu wani a cikin ‘ya’yanta da ya gaje ta a wannan sana’a ta waka? Sai Salmai ta ce, ko kusa babu wani daga cikin yaranta su bakwai da ta haifa da ya nuna sha’awar harkar waka, hasali ma mafi yawancinsu tuni sun yi aure; sun tare a gidajen mazajensu, amma dai a cewar tata; har yanzu idan aka kunna wakokinta a gidajen rediyo, hakan na matukar saka ta farin ciki tare da tuna mata shekarun kuruciyarta.

A zamanin baya, gwamnatoci sun yi amfani da wakoki da sauran hanyoyi wajen wayar da kan mutane, musamman wadanda ke zaune a karkara, domin nusar da su muhimmancin neman ilimin addini da na boko, tsabtace wajen muhallinsu da kuma hanyoyin da za su bi wajen kare kansu daga wasu cututtuka daban-daban a wancan lokaci.

Salmai
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Mutane Da Dama Sun Jikkata Yayin Da Tanka Ta Yi Bindiga A Abuja

Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Bindigar Tankar Mai A Enugu

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.