• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Labarai
0
Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki kuma, shugaban karamar hukumar Jibiya a jihar Katsina Hon. Bishir Sabiu Maitan ya bayyana cewa akwai fiye da mutane 150 da ke rike a hannun masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a karamar hukumar Jibiya.

Hon. Maitan ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake yi wa wakilan kafafen yada labarai bayani irin kokarin da gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Aminu Bello Masari akan ‘yan gudun hijira da ke makarantar ‘yan mata da GGSS Jibiya.

  • Hare-Haren ‘Yan Bindiga Ya Tilasta Yara 3,000 Daina Zuwa Makaranta A Katsina

Shugaban ya kara da cewa kullum sai an kai hari a karamar hukumar Jibiya kuma kullum sai an dauki mutane da niyyar a biya kudin fansa kafin a sake su.

”Wannan al’amarin ya wuce duk inda ake tunanin sa, kusan yanzu na koma ba ni da wani aiki da wuce kula da ‘yan gudun hijira da kuma karbar rahotanni na kai hare-haren wuce gona da iri daga ‘yan bindiga, kullum maganar ke nan.”in ji shi.
Ya nunar da cewa yanzu haka akwai mutum 60 dukkansu ‘yan gari daya suna hannun ‘yan bindiga ana ta kokarin ganin yadda za a kubutar da su daga hannun masu garkuwa da mutane sai an ba da kudin fansa.

A cewarsa, “jami’an tsaro da kuma ita kanta gwamnati suna kokari sosai wajan ganin an kawo karshen wannan al’amari, amma fa idan an toshe can, sai can ya bude, Allah ya Kawo mana zaman lafiya,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Shugaban karamar hukumar dai ya ce wannan adadin da ya ambata an dauke mutanen ne a cikin wata guda kacal, sannan ya kara da cewa a haka ma an sako wasu da iyalansu da suka biya kudin fansa.

Karamar Hukumar Jibiya dai tana cikin kananan hukumomin da ‘yan bindiga suka hana sakat, inda yanzu haka fiye da mutum 20,000 na gudun hijira, wasu a Nijeriya wasu kuma a jamhuriyar Nijer.

Haka kuma aikin ‘yan bindigar ya tilasta wa da yawa daga cikin magidanta tserewa su bar iyalan su, wasu kuma tuni suka riga mu gidan gaskiya, amma babar matsalar ita ce yadda wannan al’amari ya ki ci ya ki cinyewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

Next Post

Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

9 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

11 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

13 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

14 hours ago
Next Post
Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.