• Leadership Hausa
Friday, June 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

by El-Zaharadeen Umar
11 months ago
in Labarai
0
Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki kuma, shugaban karamar hukumar Jibiya a jihar Katsina Hon. Bishir Sabiu Maitan ya bayyana cewa akwai fiye da mutane 150 da ke rike a hannun masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a karamar hukumar Jibiya.

Hon. Maitan ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake yi wa wakilan kafafen yada labarai bayani irin kokarin da gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Aminu Bello Masari akan ‘yan gudun hijira da ke makarantar ‘yan mata da GGSS Jibiya.

  • Hare-Haren ‘Yan Bindiga Ya Tilasta Yara 3,000 Daina Zuwa Makaranta A Katsina

Shugaban ya kara da cewa kullum sai an kai hari a karamar hukumar Jibiya kuma kullum sai an dauki mutane da niyyar a biya kudin fansa kafin a sake su.

”Wannan al’amarin ya wuce duk inda ake tunanin sa, kusan yanzu na koma ba ni da wani aiki da wuce kula da ‘yan gudun hijira da kuma karbar rahotanni na kai hare-haren wuce gona da iri daga ‘yan bindiga, kullum maganar ke nan.”in ji shi.
Ya nunar da cewa yanzu haka akwai mutum 60 dukkansu ‘yan gari daya suna hannun ‘yan bindiga ana ta kokarin ganin yadda za a kubutar da su daga hannun masu garkuwa da mutane sai an ba da kudin fansa.

A cewarsa, “jami’an tsaro da kuma ita kanta gwamnati suna kokari sosai wajan ganin an kawo karshen wannan al’amari, amma fa idan an toshe can, sai can ya bude, Allah ya Kawo mana zaman lafiya,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Shugaban karamar hukumar dai ya ce wannan adadin da ya ambata an dauke mutanen ne a cikin wata guda kacal, sannan ya kara da cewa a haka ma an sako wasu da iyalansu da suka biya kudin fansa.

Karamar Hukumar Jibiya dai tana cikin kananan hukumomin da ‘yan bindiga suka hana sakat, inda yanzu haka fiye da mutum 20,000 na gudun hijira, wasu a Nijeriya wasu kuma a jamhuriyar Nijer.

Haka kuma aikin ‘yan bindigar ya tilasta wa da yawa daga cikin magidanta tserewa su bar iyalan su, wasu kuma tuni suka riga mu gidan gaskiya, amma babar matsalar ita ce yadda wannan al’amari ya ki ci ya ki cinyewa.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

Next Post

Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

Related

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu
Labarai

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

3 hours ago
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata
Labarai

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

3 hours ago
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

5 hours ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

7 hours ago
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda
Labarai

Yadda Matashi Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 10 Fyade A Bauchi

8 hours ago
Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa

9 hours ago
Next Post
Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

June 2, 2023
Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

June 2, 2023
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

June 2, 2023
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

June 2, 2023
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

June 2, 2023
Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

June 2, 2023
An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

June 2, 2023
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

June 2, 2023
RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

June 2, 2023
Da Gaske Biyayya Ga Miji Tana Gaba Da Biyayaya Ga Iyaye?

Da Gaske Biyayya Ga Miji Tana Gaba Da Biyayaya Ga Iyaye?

June 2, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.