• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Cikakkun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ga Al’ummar Duniya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Samar Da Cikakkun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ga Al’ummar Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa, samar da cikakkiyen tsari na kiwon lafiya ga al’umma zai kai ga samar da al’umma masu koshin lafiya da za su iya bayar da gudmmawar su ga cigaba yankunan da suka samu kansu, a kan haka ne hukumar ta tsayu wajen gudanar da bukin ranar lafiya ta duniya da aka ware kowacce ranar 12 ga watan Disamba na kowacce shekara, wannan wata dama ce na jawo hankalin masu ruwa da tsaki a kan halin da harkar kiwon lafiya take ciki a sassan duniya.

Taken bikin wannan shekarar shi ne, “Samar Da Duniyar Da Muke Bukata: Samar Da Cikakkiyar Lafiya Ga Kowa Da Kowa.” An karfafa bukatar samar da daidaito, aiki da gaskiya da kuma muhalli mai kyau tare da zuba jari mai inganci don samar da hukumomin lafiya ingantattu da za su iya tabbatar da ganin lafiyar al’ummar duniya tana gudana ba tare da wata matsala ba.

  • Zan Bayyana Dan Takarar Da Zan Mara Wa Baya A Janairu – Wike
  • An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

Shirin samar da lafiya ga al’ummar duniya zai tabbatar da gina cibiyoyin lafiya masu inganci a sassan duniya tare da bude kofar cibiyoyin ga kowa da kowa. Samar da kiwon lafiya ga al’umma yana da nasaba ga ci gaba duniya gaba daya. A irin wannan ranar ne ana kwatanta yadda cibiyoyin lafiya suke a sassan duniya da nufin irin bambancin da ake samu a tsakaninsu don hakan ya zama darasi mahukunta ta haka za su himmatu wajen an kara bayar da kokari don samun al’umma masu cikakkiyar lafiya a sassan duniya.

Saboda muhimmancin samar da cikakkiyar kiwon lafiya ga al’ummar duniya a halin yanzu an sanya lamarin a cikin muradun karni da ake fatan cimma a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2030, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi. A kasashe da dama samar da cikakken tsarin kiwon lafiya yana neman ya fi karfin talakawa a cikin al’umma.

Babban ginshikin a tsarin samar da kiwon lafiya shi ne samar da ruwa a kan haka ne kungiyar ‘WaterAid’ ta bayar da rahoton cewa, harkar kiwon lafiya ta kasashe da dama ta rushe ne saboda yadda aka kasa samar da ingantaccen ruwan sha, haka ma an kasa samar da wutar lantarki ga al’umma yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Hakanan kuma Hukumar Lafiya ta Duniya da UNICEF sun bayar da rahoto a shekarar 2015 cewa, kashi 38 na asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da rahoton ya karkacde basu da hanyoyin samun cikakkken ruwan sha, kashi 35 kuma basu da ruwan da masu mu’amala da su za su samu isasshen ruwan da za su wanke hannu da shi don kariya daga cututtuka yadda ya kamata. Rahoton ya kuma lura da cewa, in har jami’an kiwon lafiya basu iya tsaftace harabobin asibiti yadda yakamata to kokarinsu na bayar da cikakkiyar kulawa yana cikin gargara kenan.

Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, tsarin nan na WASH wanda hukumar WHO da UNICEF ke daukar nauyi suna cikin tsarin nan na Majalisar Dinkin Duniya na ‘UN’s Global Action Plan” na tabbatar da ganin dukkan cibiyoyin kiwon lafiya a fadin duniya suna samun isashen ruwa yadda yakamata don gudanar da ayyukansu nan da shekarar 2030.

Yana kuma da muhimmanci a lura cewa, samar da ingantaccen kiwon lafiya a duniya a bu ne daya shafi kowa da kowa, kuma a wannan lokacin ne ya fiye kowanne lokaci yakamata a tabbatar da dukkan cibiyoyin kiwon lafiyarmu sana samun kulawa yadda yakamata. Cutar Korona da aka fuskanta a fadin duniya ta zama wani gwaji ga cibiyoyin kula da lafiyar mu. Hankalin shugabanin ya koma a kan bukatar tabbatar da ganin cibiyoyin kiwon lafiyan mu suna aiki yadda yakamata don fuskantar ire-iren wannan matsalar a nan gaba.

Haka kuma wasu na ganin shirin samar da kiwon lafiya kamar wani hakki ne da yakamata kowa ya samu amma wasu kuma na ganin lamarin a matsayin wata haja, saidai gaba daya lamarin samar da kiwon lafiya ga al’umma ya tashi daga wani abin da ba a dauka da muhimmanci ba zuwa wani abin da ya zama gaskiya musamman ma a kasashen duniya da suka cigaba.

Amma kuma ga wasu al’umma masu yawa, musamman na kasashe matalauta hakar sammar da kiwon lafiya harkan kamar a mafarki.

Rahoton hukumar WHO suka bayyana cewa, akalla rabin al’ummar duniya basu da zarafin samun cikakken kiwon lafiya kamar yadda shirin muradun karni SDGs ya tabbatar, da kuma kudurin majalisar dinkin duniya ya nema.

Wani lamari mai muhimmanci game da shirin samar da kiwon lafiya ga al’ummar duniya shi ne bukatar da ake yita sai mutane sun biya kudin kiwon lafiyar su wanda haka yana kara tura akalla mutum miliyan 100 ne zuwa cikin kangin talauci a duk shekara ciki kuma akwai ‘yan Afrika fiye da mutum miliyan 11.

Kashi 77.2 a cikin dari na ‘yan Nijeriya na cigaba da dogara ne da sayen magani a kemis a duk lokacin da suke fama da rashin lafiya. Shirin samar da kiwon lafiya ga al’umma yana fuskantar matsaloli iri daya musamman a Nijeriya da sauran kasashen Afrika, cikin matsalolin akwai yadda aka fuskanci matsalolin da cutar korona ta haifar musamman daga hukumomi.

Amma kuma wasu mastalolin lamari ne da ta shafi duniya gaba daya, wadanda suka hada da yadda aka rika tattara bayanai, da zuba jari da batun samar da kwararru wadanda za su yi aikin da ya kamata na ganin an cimma burin da aka sa a gaba.

Haka kuma masana sun tabbatar da cewa, in har ana son cimma shirin samar da ingataccen tsarin kiwon lafiya ga al’ummar duniya dole ne a inganta asibitocinmu, a kuma horas da ma’aikatan lafiya da kara yawan cibiyoyin kiwon lafiyar a sassan Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cibiyoyin LafiyaWHO
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gabatar Da Tambarin Musamman Da Kayan Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Na Shekarar 2023 Mai Alamar Zomo

Next Post

Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

7 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

12 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

14 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

17 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

21 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

22 hours ago
Next Post
Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.