• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Cikakkun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ga Al’ummar Duniya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Samar Da Cikakkun Cibiyoyin Kiwon Lafiya Ga Al’ummar Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa, samar da cikakkiyen tsari na kiwon lafiya ga al’umma zai kai ga samar da al’umma masu koshin lafiya da za su iya bayar da gudmmawar su ga cigaba yankunan da suka samu kansu, a kan haka ne hukumar ta tsayu wajen gudanar da bukin ranar lafiya ta duniya da aka ware kowacce ranar 12 ga watan Disamba na kowacce shekara, wannan wata dama ce na jawo hankalin masu ruwa da tsaki a kan halin da harkar kiwon lafiya take ciki a sassan duniya.

Taken bikin wannan shekarar shi ne, “Samar Da Duniyar Da Muke Bukata: Samar Da Cikakkiyar Lafiya Ga Kowa Da Kowa.” An karfafa bukatar samar da daidaito, aiki da gaskiya da kuma muhalli mai kyau tare da zuba jari mai inganci don samar da hukumomin lafiya ingantattu da za su iya tabbatar da ganin lafiyar al’ummar duniya tana gudana ba tare da wata matsala ba.

  • Zan Bayyana Dan Takarar Da Zan Mara Wa Baya A Janairu – Wike
  • An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

Shirin samar da lafiya ga al’ummar duniya zai tabbatar da gina cibiyoyin lafiya masu inganci a sassan duniya tare da bude kofar cibiyoyin ga kowa da kowa. Samar da kiwon lafiya ga al’umma yana da nasaba ga ci gaba duniya gaba daya. A irin wannan ranar ne ana kwatanta yadda cibiyoyin lafiya suke a sassan duniya da nufin irin bambancin da ake samu a tsakaninsu don hakan ya zama darasi mahukunta ta haka za su himmatu wajen an kara bayar da kokari don samun al’umma masu cikakkiyar lafiya a sassan duniya.

Saboda muhimmancin samar da cikakkiyar kiwon lafiya ga al’ummar duniya a halin yanzu an sanya lamarin a cikin muradun karni da ake fatan cimma a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2030, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi. A kasashe da dama samar da cikakken tsarin kiwon lafiya yana neman ya fi karfin talakawa a cikin al’umma.

Babban ginshikin a tsarin samar da kiwon lafiya shi ne samar da ruwa a kan haka ne kungiyar ‘WaterAid’ ta bayar da rahoton cewa, harkar kiwon lafiya ta kasashe da dama ta rushe ne saboda yadda aka kasa samar da ingantaccen ruwan sha, haka ma an kasa samar da wutar lantarki ga al’umma yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

Hakanan kuma Hukumar Lafiya ta Duniya da UNICEF sun bayar da rahoto a shekarar 2015 cewa, kashi 38 na asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da rahoton ya karkacde basu da hanyoyin samun cikakkken ruwan sha, kashi 35 kuma basu da ruwan da masu mu’amala da su za su samu isasshen ruwan da za su wanke hannu da shi don kariya daga cututtuka yadda ya kamata. Rahoton ya kuma lura da cewa, in har jami’an kiwon lafiya basu iya tsaftace harabobin asibiti yadda yakamata to kokarinsu na bayar da cikakkiyar kulawa yana cikin gargara kenan.

Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, tsarin nan na WASH wanda hukumar WHO da UNICEF ke daukar nauyi suna cikin tsarin nan na Majalisar Dinkin Duniya na ‘UN’s Global Action Plan” na tabbatar da ganin dukkan cibiyoyin kiwon lafiya a fadin duniya suna samun isashen ruwa yadda yakamata don gudanar da ayyukansu nan da shekarar 2030.

Yana kuma da muhimmanci a lura cewa, samar da ingantaccen kiwon lafiya a duniya a bu ne daya shafi kowa da kowa, kuma a wannan lokacin ne ya fiye kowanne lokaci yakamata a tabbatar da dukkan cibiyoyin kiwon lafiyarmu sana samun kulawa yadda yakamata. Cutar Korona da aka fuskanta a fadin duniya ta zama wani gwaji ga cibiyoyin kula da lafiyar mu. Hankalin shugabanin ya koma a kan bukatar tabbatar da ganin cibiyoyin kiwon lafiyan mu suna aiki yadda yakamata don fuskantar ire-iren wannan matsalar a nan gaba.

Haka kuma wasu na ganin shirin samar da kiwon lafiya kamar wani hakki ne da yakamata kowa ya samu amma wasu kuma na ganin lamarin a matsayin wata haja, saidai gaba daya lamarin samar da kiwon lafiya ga al’umma ya tashi daga wani abin da ba a dauka da muhimmanci ba zuwa wani abin da ya zama gaskiya musamman ma a kasashen duniya da suka cigaba.

Amma kuma ga wasu al’umma masu yawa, musamman na kasashe matalauta hakar sammar da kiwon lafiya harkan kamar a mafarki.

Rahoton hukumar WHO suka bayyana cewa, akalla rabin al’ummar duniya basu da zarafin samun cikakken kiwon lafiya kamar yadda shirin muradun karni SDGs ya tabbatar, da kuma kudurin majalisar dinkin duniya ya nema.

Wani lamari mai muhimmanci game da shirin samar da kiwon lafiya ga al’ummar duniya shi ne bukatar da ake yita sai mutane sun biya kudin kiwon lafiyar su wanda haka yana kara tura akalla mutum miliyan 100 ne zuwa cikin kangin talauci a duk shekara ciki kuma akwai ‘yan Afrika fiye da mutum miliyan 11.

Kashi 77.2 a cikin dari na ‘yan Nijeriya na cigaba da dogara ne da sayen magani a kemis a duk lokacin da suke fama da rashin lafiya. Shirin samar da kiwon lafiya ga al’umma yana fuskantar matsaloli iri daya musamman a Nijeriya da sauran kasashen Afrika, cikin matsalolin akwai yadda aka fuskanci matsalolin da cutar korona ta haifar musamman daga hukumomi.

Amma kuma wasu mastalolin lamari ne da ta shafi duniya gaba daya, wadanda suka hada da yadda aka rika tattara bayanai, da zuba jari da batun samar da kwararru wadanda za su yi aikin da ya kamata na ganin an cimma burin da aka sa a gaba.

Haka kuma masana sun tabbatar da cewa, in har ana son cimma shirin samar da ingataccen tsarin kiwon lafiya ga al’ummar duniya dole ne a inganta asibitocinmu, a kuma horas da ma’aikatan lafiya da kara yawan cibiyoyin kiwon lafiyar a sassan Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cibiyoyin LafiyaWHO
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gabatar Da Tambarin Musamman Da Kayan Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Na Shekarar 2023 Mai Alamar Zomo

Next Post

Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

14 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

17 hours ago
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

18 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

19 hours ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

20 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

24 hours ago
Next Post
Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.