• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Ingantattun Bayanan Kidaya Sirri Ne Na Kyakkyawan Ci Gaba – Ganduje

by Mustapha Ibrahim
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Samar Da Ingantattun Bayanan Kidaya Sirri Ne Na Kyakkyawan Ci Gaba – Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yace samar da cikakkun bayanan kididdigar Jama’a, wata dama ce ta samar da ci gaba, sannan kuma duk wat aGwamnati mai kyakkyawan hange samun nasara, ya zama wajibi ta san adadin al’ummar da ke bukatar ababan more rayuwa akowa ne bangare, kamar haske nwutar lantarki, ruwan sha, gidaje, harkar Lafiya da Ilimi.

Kamar yadda Daraktan yada labaran Ofishin Mataimakin Gwamnan Hassan Musa Fagge ya Shaida wa LEADERSHIP Hausa.

  • Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen
  • 2023: Ana Rububin Kujerar Ahmed Lawan Bayan Soke Takararsa

“Kidaya wani gimshiki ne na gina wa tare da samar da zorewar ci gaba” In ji shi Gwamnan wanda mataimakinsa kuma dan takarar Gwamna na Jam’iyyar APC Dakta Nasiru Yusif Gawuna ya wakilta, Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a wurin taron masu ruwa da tsaki kan shirin Kidayar Shekara ta 2023 da kuma Kidayar Gidaje mai taken “Kidayar Shekara ta 2023- Tabbatar da shigar da Jama’a cikinta” wanda aka gudanar a babban dakin taro na Coronation da ke Fadar Gwamnatin Jihar Kano.

“Dukkanin al’umma wakilai ne kuma wadanda zasu amfana da wannan mataki ne, saboda haka ilimin shirin Kidaya ta Kasata fuskar fadin Kasa, kasafi da fannonin tsumi da tanadi duk ana bukatarsu wajen tsare tsaren gudanar da Kidaya wanda hakan wani tubali ne na aiwatar da harkokin Gwamnati.”

“Mun Gamsu kwarai da samarda kayan aikin irin na zamani wanda Hukumar Kidayar ta samar domin tabbatar gudanar da kidayar ta hanyar zamani a Nijeriya wanda hakan zai tabbatar da samun ingantattun bayanai.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

“Ya ci gaba cewa, Gwamnatinmu na bukatar sabbin kunshin bayanai wanda zai tabbatar da aiwatar da sabunta dokokin kidayar domin dorewar ci gaba da sauran tsare tsaren Gwamnati ga kowane bangare na al’umma.

A cewarsa, Jhar Kano muna minta da cewar Hukumar kidayar na da karfi kuma a shirye take wajen tabbatarwa da Kasar nan Ingantacciyar Kidaya wadda kowazai gamsu da ita a Shekara ta 2023.

Gwamnan ya tabbatar da samun goyon bayan Gwamnati tare da Jajircewa domin tabbatar da nasarar gudanar da kidayar domin amfanin al’umma baki daya.

Kwamishinan Hukumar kidayar na Kasa reshen Jihar Kano Dakta Isma’ila Lawal Sulaiman ya bayyana cewa babbar nasarar da ake fatan samu kan kidayar shi ne gudanar da Ingantacciyar kidaya kuma karbabbaya wanda zata sake fasali tare da kai wa ga ingantaccen Matsayi kamar na kasaahen duniya, don haka akwai bukatar shigowar dukkanin masu ruwa da tsaki domin samun kyakkyawan sakamakon bayanai wanda zasu gamsar da matakin da ake bukata.

Cikin wadanda Suka halarci taron akwai ‘yan Majalisar zartarwar Jihar Kano, Sarakunan Gargajiya, kungiyoyin Mata da matasa, abokan mu’amala da kungiyoyi masu zaman kansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abubuwan More RayuwaGandujeJin Dadin Al'ummakanoKidayaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bai Wa Hukumomin Alhazai Na Jihohi ‘Yanci Zai Taimaka Wajen Inganta Aikin Hajji – Barista Abdullahi

Next Post

Bai Kamata A Maida Iraki Fagen Takarar Siyasa Tsakanin Bangarori Daban-daban Ba -In Ji Kasar Sin

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

19 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Bai Kamata A Maida Iraki Fagen Takarar Siyasa Tsakanin Bangarori Daban-daban Ba -In Ji Kasar Sin

Bai Kamata A Maida Iraki Fagen Takarar Siyasa Tsakanin Bangarori Daban-daban Ba -In Ji Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.