ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar ‘Yan Siyasa Su San Kalaman Da Za Su Furta Lokacin Kamfen

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
'Yan Siyasa

Da akwai bukatar sai ‘yan siyasa sun kai zuciyarsu nesa wajen barin yin amfani da kalaman da ba su dace ba, lokacin da suka je yakin neman zabe.

Irin hakan shi ne yake harzuka zuciyar magoya wani dan takara, bayan wasu na wani dan takarar sun furta kalaman da ba su dace ba.

  • Ranar Abokan Hulɗa: NIS Ta Karrama Jami’anta Masu Aiki Tuƙuru
  • Za Mu Yi Nazarin Hukuncin Kotun Daukaka Kara – ASUU

Wannan an fi samun hakan ne idan ‘yan takarar mukami daya suka zo yin kamfen a garin dan takarar da yake adawa ba domin komai ba, sai saboda duk mukami daya suke nema, amma jam’iyyun da suke matakara sun bambanta. Bugu da kari kuma idan suna takarar kujera daya kamar dai yadda na fara yin bayani nan nema abin aka fi samun matsala, a irin wannan yanayi, amma kuma wannan idan duk an kai zuciya nesa ba wani abu ba ne.

ADVERTISEMENT

Allah ai shi ke ba da mulki ga wanda ya so don haka komai nacin mutum duk wadansu hanyoyin da zai bi domin yin hakan, idan lokacin shi bai yi babu yadda zai yi.‘Yan takarar mukaman siyasa daban- daban ya dace su sanc ewa duk wani abin da ya faru ko na kirki ko akasin haka, lokacin yakin neman zabe, ana ta’allaka irin hakan ne da cewa sune sanadiyar faruwar al’amarin na tashin hankali.

Domin kuwa wani dan takarar ma tsoro yake da shakkun zuwa wurin da ya dace ya je yakin neman zaben, ba domin komai  ba sai don gudun abinda zai iya faruwa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ko da yake dai ba a taru aka zama daya ba, sai dai kuma wani al’amari ba a rasa nono a riga.

Wasu daga cikin ‘yan takarari dan za su tafi kamfen wani gari, ba suyin taka- tsantsan da irin kalaman da suka dace su yi. Amma duk da sanin cewar kalaman batanci lokacin yakinn eman zabe ba su kamata, sai dai kuma wasu ‘yan siyasar harshirin yin hakan suke yi.

Sunaganin tamkar yin hakan zai kara masu wani kwarjini daga wurin jama’a. Ranar Laraba ta wannan makon ce aka fara gangami na kamfen din siyasa inda akes a ran dukkan ‘yan takarar Shugaban kasa 18, za su shigayin kamfen din.

Haka nan ma ‘yan takarar majalisu nDattawa da na Tarayya, duk cikin wannan watan ne za su fara. Masu takarar gwamna da ‘yan majalisar Jiha su sai 10 gawatan Oktoba 2022.

Wannan shi yasa hukumomi wadanda suka hada da hukumar zabe mai zaman kanta, hukumar kula da harkokin gidajen yada labarai da suka shafi Talabijin da Rediyo, cibiyar horar da ‘yan majalisa ta kasa.

Duk dai maganar daya ce ta yin nesa nesa da kalaman batanci irin wadanda ka iya harzuka magoyabaya, su kai garungumar tashin hankali, wanda ba shi ne ake bukata ba a wannan lokaci da ake fama da tabarbarewar tsaro.

Ita ma majalisar zaman lafiya ta kasa karkashin Shugabancin tsohon Shugaban kasa na mulkin soja ritaya Janar Abdulsalam Abubukar tare da wasu mashahuran mutaned a suka hada da Alhaji Aliko Dangote Bishop Hassan Kuka ba a bar ta a baya ba wajen yin hakan. Saboda kuwa za su yi taro ranar Alhamis duk da zummar jawo hankalin ‘yan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki, ganin an fara yakin neman zabe a guiji furta kalaman da ba su kamata.

'Yan Siyasa
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Shugabanci A Kasuwanci (2)

Shugabanci A Kasuwanci (2)

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.