• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bukukuwan da aka gudanar na ranar abinci ta duniya kwanan nan sun isa su jawo hankalin gwamnati da al’ummar kasashen duniya a kan matsalar abinci da ake fuskanta a Nijeriya dama wasus assan duniya, wannan ya zama dole ne musamman ganin matsalar da aka fuskanta sakamakon annobar cutar Korona da kuma matsalar dumamar yanayi a duniya da kuma ambaliyar ruwar da aka fuskanta, ana wannan bikin ne a fadin duniya, ranar da ta yi daidai da ranar da aka kafa kungiyar nan ta Majalisar Dinkin Duniya ta UNFAO a shekarar 1945, bikin na da matukar muhimmanci don a wannan ranar ce al’ummar duniya ke haduwa don tattaunawa a kan matsalar da ake fuskanta ta karancin abinci ko kuma rashin abinci gaba daya a wasu sassan duniya.

Kamar dai yadda shirin samar da abinci a duniya (WFP) ya sanar, shekarar 2022 ta zamar wa al’ummar duniya wata fage na fuskantar matsaloli da suka shafi yanayin samar da abinci wadanda suka hadada rikice-rikice kamar abin da ke faruwa a yakin Rasha da Yukrain da lamarin dumamar yanayi da hauhawar farashin kayan masarufi haka nan kuma tayar da jijiyar wuya a tsakanin kasashe yana kara haifar da yanayin da noma zai gagara wanda hakan zai ka gai haifar da matsalolin abinci.

  • Xi Ya Taya Murnar Shirya Bikin Liyafar Shekara-Shekara Ta Kwamitin Huldar Amurka Da Sin
  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Tsohon Sakataren Gwamnatin Enugu Da Wasu

Wadannan matsalolin suntaimaka wajen haifar da rashin abinci irin wanda ba a taba gani irin shi ba atarihi.

Ra’ayin wannan jaridar si ne, an dade ana ta surutu a kan bukatar samar da yanayin da al’umma duniya za su samu damar samun ingantaccen abinci mai gina jiki.

A wannan mahangar muke jinjina da godiya da taken bikin na wannan shekarar wanda yake kamar haka, “Tafiya TareDa Kowa Da Kowa Don Samar Da Ingantaccen Abinci Mai Gina Jiki.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Taken na wannan shekarar ya nuna muhimmancin hadin kai a tsakanin al’ummar duniya don karfafa tsarin samar da abinci a fadin duniya gaba daya.

Wannan ba tare da wata tantama ba suna cikin manyan matsalolin da al’ummar duniya ke fuskanta, cikin su kuma akwai talauci, rashin lafiya dalalacewar muhalli.

Don kawo karshen wannan matsalar a fadin duniya ara’ayinmu dole a samar da wani tsari da zai tafi tare da dukkan al’umma ba tare da nuna banbanci ba domin ai dukkan al’ummar duniya na da muhimmanci wajen samun nasarar wannan aikin.

A kan haka ne dole Gwamnati, Kamfanoni masu zaman kansu da Malaman jami’o’i da kungiyoyi masu zaman kansu da sauran daidaikun mutane su yi aiki tare da juna don samar da yanayin da kowa zai samu abinci cikin kwanciyar hankali ba tare da wata mastala ba.

Abin takaici ne a ra’ayinmu, duk da kokarin da ake yi na samar da ingantacciyar al’umma har yanzu mutane da dama a baya ba a tafiya da su, sun kasa cin gajiyar ci gaba da aka samu na kimiyya da fasaha a bangaren tattalin arziki da ta zamantakewa.

Abayyane lamarin yake, duniya nada  abinci da al’ummar duniya za su iya ci ba tare da matsala ba amma kuma miliyoyin mutane a fadin duniya na kwana da yunwa wasu kuma ba su da ikon samun abinci mai gina jiki.

Muna kara jaddada cewa, annobar cutar Korona, Dumamar yanayi da mamayar kasar Yukrain da Rasha ta yi ya kawo cikas ga kokarin samar da ingantaccen abinci ga al’umma duniya da kuma shirin kawar da yunwa a fadin duniya.

Kididdiga ya nuna cewa, kasha 75 na mutanen da suke fuskantar matsalar abinci mutane ne da suka dogara da harkar noma a matsayin hanyar samun abincin su, su ne kuma suka fi dandanawa sakamakon da annobar da dan adam ya haifar wakansa yake kawowa, haka kuma sune suka fi fukantar rikice-rikicen da suka hada da na kabilanci da nuna banbanci a tsakanin maza da mata, wadannan mutanen na matukar bukatar tallafin kudade da kayan aikin noma na zamani don su samu hanyoyin samar da abinci ga al’ummarsu.

A daidai wannan rana ta abinci ta duniya, ya zama dole musamman ganin irin matsalolin da ake fuskanta a sassan duniya duniya su hada hannu don fuskantar matsalar ba tare da nuna banbanci ba, a kan haka ne dukkan bangarori na rayuwar al’umma suna da gudummawar da ya kamata su bayar don samar da abinci ingantacce da zai samar wa al’umma cikakkiyar lafiya.

Bincike ya nuna cewa, a shekafrar2021 misali, an kiyasta cewa kasha 29.3 na al’ummar duniya kusan mutum Biliyan 2.3 na fuskantar tsanani ko tsaka tsakanin matsalar abinci, haka kuma kashi 11.7 na al’umma duniya kusan mutum Biliyan 923.7 na fuskantar kololuwar tsananin matsalar abinci.

Haka kuma banbancin da ake samu a tsakanin jinsin mata da maza a kan yadda suke samun abinci yana kara fadadaa kullum.

A shekarar 2021, kasha 31.9 na mata a duniya na fuskantar matsanancin rashin abinci in aka kwatanta da kashi 27.6 na maza.

Rahoton ya kuma bayyana cewa a shekarar 2020, an kiyasta cewa kasha 22 na yara da basu gaza da shekara 5 suna fuskantar matsanancin rashin abinci, yayin da kashi 6.7 na yaran rashin abincin ya yi musu illa wasu kashi 5.7 na yaran kuma suna fuskantar cutar kiba saboda ciye-ciye marasa kangado.

Rahoton ya kuma kiyasata cewa, fiye da mutum miliyan 670 a fadin duniya za su fuskanci rashin abinci a cikin shekarar 2030 zuwa 2038, haka lamarin yake a shekarar 2015 a lokacin da aka kaddamar da shirin samar da abinci ga al’ummar duniya nan da shekarar 2030.

Mutum fiye da Miliyan 828 aka tabbatar sun fuskanci yunwa a shekarar 2021.

Bincike ya kuma nuna cewa daya daga cikin magidanta 8 a duniya na fuskantar cutar kiba a kusan dukkan bangarorin duniya ciki har da kasashe masu tasowa.

Ga Nijeriya kuwa harkokin ‘yan ta’adda yana kara tayar da hankalin al’umma game da shirin samar da abinci sai kuma ga gaggarumar ambaliyar ruwar da ta share filayen noma masu yawa.

Ra’ayinmu a nan shi ne na bukatar gwamnati ta kawo dauki ga manoman da suka yi asara a sassan Nijeriya. Dole a gaggauta kawar da al’amarin da muke tsoron aukuwarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiKoronaMalaman Jami'o'iRa'ayi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 30 Sun Mutu Cikin Mako Daya A Hatsarin Mota A Kwara

Next Post

Hasashen Harin Ta’addanci A Abuja: Kalaman Amurka Da Ingila Sun Jefa Mutane Rudani

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

8 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

10 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

17 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

17 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

20 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Hasashen Harin Ta’addanci A Abuja: Kalaman Amurka Da Ingila Sun Jefa Mutane Rudani

Hasashen Harin Ta'addanci A Abuja: Kalaman Amurka Da Ingila Sun Jefa Mutane Rudani

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.