• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Zama Muhimmin Aikin Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ya Zama Muhimmin Aikin Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana a yau Alhamis cewa, Sin da Afirka suna daukar matakai na tinkarar sauyin yanayi, da sa kaimi ga samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

Yayin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ke ziyara a wasu kasashen Afirka, ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan ci gaban kasashen Afirka ba tare da gurbata muhalli ba, da yin kokari tare, wajen sa kaimi ga zamanintar da kasa, tare da kiyaye muhalli, da sada zumunta da juna.

  • Da Gaske Ne Amurka Tana Kare ‘Yancin Fadin Albarkacin Baki?
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram Da Dama A Harin Da Suka Kai A Fadar Shugaban Kasar Chadi

Guo Jiakun ya kara da cewa, kasashen Afirka sun koyi fasahohin Sin a fannin dashen shingayen kare karfin iska na Sanbei, sun kaddamar da shirin dasa bishiyoyi na nahiyar Afirka, don daidaita matsalolin kwararar hamadar Sahara.

A fannin makamashi mai tsabta kuwa, kasar Sin ta aiwatar da daruruwan ayyuka a nahiyar Afirka. An shigar da fasahar noman ciyawar kasar Sin wato Juncao cikin nahiyar Afirka, aikin da ya zama kyakkyawan misali na hadin gwiwar Sin da Afirka kuma mai matukar amfani. Hakazalika kuma, ayyukan fasahohin samar da wutar lantarki ta karfin iska, da zafin kasa, da hasken rana, sun taimakawa kasashen Afirka wajen canja tsarin samar da makamashi.

Guo Jiakun ya kara da cewa, a nan gaba, za a aiwatar da ayyukan samar da makamashi mai tsabta guda 30 a nahiyar Afirka, da gina dakunan gwaji na hadin gwiwa guda 30, da yin hadin gwiwa a fannonin harba tauraron dan Adam, da binciken duniyar wata, da sararin samaniya da sauransu. Ya ce samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, ya zama muhimmin aikin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka. (Zainab Zhang)

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Chadi Ya Gana Da Wang Yi

Next Post

Uwa Da Ɗanta Sun Ƙone Ƙurmus A Wata Gobara Abuja

Related

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

15 minutes ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

1 hour ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

2 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

4 hours ago
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

1 day ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

1 day ago
Next Post
Uwa Da Ɗanta Sun Ƙone Ƙurmus A Wata Gobara Abuja

Uwa Da Ɗanta Sun Ƙone Ƙurmus A Wata Gobara Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.