• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sana’o’i Bakwai Da Suka Fi Kawo Kudi A Nijeriya

by Sani Anwar
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan zamani da muke ciki, akwai wasu manyan sana’o’i bakwai da ake ganin sun fi taimakawa wajen saurin kawo wa mutane kudi a Nijeriya, wadannan kuwa su ne kamar haka:

Cinikin Gidaje
Sana’ar cinikin gidaje, na daya daga cikin manyan hanyoyin samun kudadade cikin sauki, musamman a wannan kasa da muke ciki. Domin kuwa, za ka iya sayen gida ka bayar da shi haya ko kuma sayen fili ka gina; daga bisani kuma ka sayar.

Wannan ne yasa wasu ke ganin babu abin da ya kai wannan sana’a tabbas da kuma samun kudaden shiga, sakamakon tsananin bukatar da ake da ita a bangaren matsuguni a daidai wannan lokaci, musamman ganin yadda gidajen haya ke matukar wahala; sakamakon rashin gina gidajen da ba a yi yanzu, saboda tsadar kayan gini da sauran makamantansu.

Noma
Babu shakka, bangaren harkokin noma a Nijeriya na ci gaba da habaka da kuma bunkasa. Wannan dalili ne yasa ake kara samun damammaki a wannan bangare da kuma samun bunkasuwar arziki.
Don haka, duk mai bukatar hanyoyin samun kudade masu yawan gaske; wajibi ne ya gaggauta rungumar wannan hanya ta noma a Nijeriya.

Kamfanin Makamashin Hasken Rana
Har ila yau, sanya hannun jari ko kafa kamfanin samar da makamashi ta hanyar hasken rana (Solar Farm), na daya daga cikin kasuwancin da yake matukar taimaka wa mutane a daidai wannan lokaci, wajen samun arziki ko kudade masu dimbin yawa a wannan zamani da muke ciki.

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Kafa wannan kamfani ta hanyar amfani da makamashin hasken rana, na taimakawa wajen samar da hasken wutar lantarki tare da rarraba ta; ta hanyar sayar wa da masu bukata a samu kudi nan take.
Shakka babu, wannan hanya ce wadda a halin yanzu; musamman ganin yadda wutar lantarki ke matukar wahalar samuwa, mutane da dama sun raja’a wajen mayar da hankali; domin amfani da wannan makamashi, don samun wutar lantarki; wanda hakan ke matukar taimaka wa masu wannan sana’a wajen samun kudade masu yawan gaske.

Harkokin Cinikayya
Kasuwanci, wanda ya kunshi saye da sayar da abubuwa kamar man fetir, gwal ko zinare da kuma kayayyakin amfanin gona; na da matukar riba, amma na bukatar sani tare da fahimtar harkokin yadda ya kamata da kuma juriya.

Har ila yau, wannan kasuwanci na matukar garawa a wannan kasa tare da bayar da damar samun makudan kudade ga wadanda ke aiwatar da sana’ar.

Shi yasa duk wanda ka ga yana aiwatar da wannan kasuwanci na sayar da zinare ko sayar da mai, ba karamin attajiri ba ne, saboda sana’a ce mai matukar bukatar da isasshen jari.

Sayen Hannun Jari
A wannan gaba, sanya hannun jari; wata hanya ce da take da tabbas, sakamakon kulawa da gwamnati ta bai wa harkar tar da rage barazanar yiwuwar samun asara a cikinta. Sannan, ana kayyade adadin yawan abin da za a samu bayan tsawon wani lokaci da aka diba wa harkar.

Shi yasa, mutane da dama ke kutsawa cikin wannan kasuwa; ba tare da wani jin tsoro ba, ganin yadda harkar ke kawo kudi tare kuma da karancin yiwuwar tafka asara a cikinta.

‘Yan Nijeriya da dama, na aiwatar da wannan kasuwanci tare da samun makudan kudade lokaci bayan lokaci a fadin wannan kasa da muke ciki a saukake.

Kudaden Da Kwararru Ke Sarrafawa
A nan, wata kasuwa ce da wasu kwararru ke sarrafa nau’o’in kudade daban-daban, dangane da yadda kasuwar hada-hadar kudaden ke juyawa. Sannan, wannan kasuwanci; baya bukatar mai aiwatar da shi ya rika zurfafa bincike a cikinsa.

Manajojin asusun, su ne ke yin wannan bincike tare da tafiyar maka da hada-hadar kasuwancin, kai kana zaune abinka. Kazalika, abin da kawai kai ake bukata a wajenka shi ne; zuba wannan hannun jari a cikin kudaden da ake hada-hadarsu tare da duba ribar da kake samu ta yau da kullum.

Ajiyar Kudi Zuwa Wani Kayyadadden Lokaci
wannan na daya daga cikin hanyoyi masu sauki na samun kudi a huce da sunan kasuwanci. Abin da kawai ake nema a nan shi ne, mai sha’awar wannan kasuwanci; ya zuba jarinsa a kamfani, sannan ba zai waige shi ba; har sai bayan wa’adin lokacin da aka diba ya cika.

Babu shakka, wannan kasuwanci na da matukar riba; sannan kuma babu asara ko kadan a cikinsa, domin kuwa za a iya samun ribar da ba a taba tsammani ba; kamar yadda tsarin kasuwancin yake.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: rayuwa mai juyiSana'ar zamaniTsadar kayan abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hakkin Bil Adam Gata Ne Ga Wasu A Amurka Karkashin Ra’ayin Wariyar Launin Fata

Next Post

Ministocin Tsaron Sin Da Amurka Sun Gana A Kasar Singapore

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

6 days ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
Ministocin Tsaron Sin Da Amurka Sun Gana A Kasar Singapore

Ministocin Tsaron Sin Da Amurka Sun Gana A Kasar Singapore

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.