ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

by Bello Hamza
1 year ago
NPA

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta bayyana cewa, ta yi hasashen Tarawa Gwamnatin Tarayya kudaden shiga Naira tiriliyan 1.28, a shekarar 2025.

Shugaban Hukumar ta NPA Abubakar Dantsoho, ya sanar da haka a ranar Litinin a babban birnin tarayar Abuja.

  • Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
  • Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Dantsoho, ya sanar da haka ne, a lokacin da ya bayyana a zaman da Kwamitin Majalisar wakilai da ke lura da al’amuran harkokin Jiragen Ruwa.

ADVERTISEMENT

A cewar Dantsoho, kaso 40 a cikin dari na kudaden shigar da ake son Tarawa, za su haura Naira biliyan 894.8, da Hukumar ta yi, hasashen tarawa, a shekarar 2024.

Shugaban ya kara da cewa, Hukumar ta NPA ta yi kasafin sama da wannan adacin, wanda kuma take son tarawa, musamman domin ta kara inganta ayyukanta, wadanda kuma za yi dai, dai da yadda ake gudanawar a fadin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA, ta yi kasafin da dara haka, na wannan adadin, musaman ganin cewa, ta na burin, kara inganta ayyukanta, yadda za su yi dai-dai, da yadda ake gudanar da ayyukan, a sauran Tashoshin Jiragen Ruwa na duniya.

Shugaban Hukumar ya kuma sanar da cewa, a shekarar 2024, Hukumar ta NPA, kudin shigar da ta yi hasashen Tarawa daga na Naira biliyan 865.39, sun karu zuwa Naira biliyan 894.86.

“ Wannan ya nuna yadda Hukumar ta NPA, ta mayar da hankali da kuma kara zage Damtse wajen ganin ta Tarawa Gwamnatin Tarayya kudaden shiga, masu yawa,”  A cewar Dantsoho.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, kudaden shigar da Hukumar ke hasashen Tarawa a shekarar ta 2025, za ta samar da su ne, daga harajin da take karba daga gun Jiregen Ruwan da aka yo jigar kaya wanda ya kai Naira biliyan 544.06 da Naira biliyan  413.06 na Jiragen Ruwa da kuma wasu sauran kudade na Naira biliyan 249.69 sai kuma kudaden shiga, na sasehn gudnar da mulki, da suka kai Naira biliyan  73.07.

Shi kuwa a na sa jawabin, a zaman na Kwamitin, Shugaban Kwamitin Nnolim Nnaji, ya yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta kara kaimi kan nasarorin da ta samar, tare da kuma kara inganta kayan da take gudanar da ayyukanta, musaman ta kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara samar da hanyoyin  ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan.

Nnaji ya sanar da cewa, Hukumar ta NPA, ta kasance wata ginshike ce, wajen bayar da gagarumar gudunmawa na kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

Shugaban ya kuma bukaci Hukumar da kara mayar da hankali, kan burukan da take son cimma duka manyan kalubalen da take fuskanta.

“Babu kata kasa a fadin duniya da za ta iya samar da wani ci gaba mai dorewa, ba tare da yin aiki, da sanarorin da Hukumar Jiragen Ruwa, ke samarwa ba,” Inji Shugaban.

 

Ya ci gaba da

“Hukumomin Jiragen Ruwa na kowacce kasa a fadin duniya, sune kashin bayan ci gaban tattalin arzikin kasa, musamman kan yadda ake gudanar da hada-hadar fitar da kaya da kuma shigar da su,” A cewar Nnaji.

Kazalika, Shugaban Kwamitin ya sanar da cewa, namijin kokarin da Hukumar ta NPA take kan yi, abin yabawa ne, kuma hakan, zai kara taimaka wa, wajen kara samar da ayyukan yi, a kasar nan.

“Hukumar ta NPA, ba wai kawai tana aikin tara kudaden shiga ba ne, ta kasance wata babbar kadara ce, wajen samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da kuma kara habaka, tattalin arzikin kasar,” Inji Shugaban.

Nnaji ya bayyana cewa, wannan Kwamtin na jiran ya ga dabarun da Hukumar za ta yi amfani da su, musamman domin kara bunkasa kudaden shigar da kuma kara samar da damar ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan, ta hanyar kasafin kudinta, na shekarar  2025.

NPA
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.