• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Gaidam

Tsohon Gwamnan jihar Yobe, kuma Sanata mai wakiltar shiyya ta daya (Zone A) a zauren majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ibrahim Gaidam tare da hadin gwiwa da Hukumar bunkasa yankunan kan iyakoki ta kasa: Border Communities Development Agency (BCDA)- sun kaddamar da tallafin kayan kiwon Kifi da sana’o’in dogaro da Kai ga matasa da mata sama da 400.

Da ya ke kaddamar da raba tallafin babban dakin taron karamar hukumar Damaturu, a babban birnin jihar Yobe, ranar Asabar, Sanata Gaidam wanda Muhammad Kiwata ya wakilta ya ce wannan kokari domin tallafa wa al’ummar mazaba da kayan sana’o’i hadi da horar da mata da Matasa, suna daga cikin abubuwan da Sanata Gaidam ke yi don kawar da zaman kashe wando domin samar da sana’a don jama’a su dogara da kansu.

  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

Gaidam ya ce ya zama wajibi a matsayin su na shugabannin al’umma su tashi tsaye wajen samarwa da mata da matasa ayyukan yi musamman sana’o’in dogaro da kai, bayar da horo tare da tallafa musu da abubuwan da za su fara sana’o’in a lokacin da suka kammala samun horon.

Ya ce, “Saboda haka ne, ta hanyar hadin gwiwar fadar shugaban kasa mu ka yi kokarin bayar da tallafin wadannan kayan fara sana’o’i ga matasanmu sama da 400; domin kiwon Kifi wanda hakan zai taimaka su tsaya da kafafunsu.”

A nashi bangaren, babban jami’in Hukumar BCDA, Mista Rotimi Taiwo ya bukaci matasan su yi amfani da kayan da aka raba musu ta hanyar da ta dace, tare da sanar dasu cewa jami’an hukumar zasu biyo sawu domin tabbatar da cewa matasan basu sayar da kayan ba. Ya yi barazanar mika duk wanda aka kama da sauya akalar kayan zuwa hukumar EEFC.

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Wakilinmu ya zanta da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daga karamar hukumar Yunusari, Fusama Alhaji Bai inda ya bayyana cewa, sun yaba matuka dangane da wannan tallafin da suka samu na gwamnatin Tarayya ta hanyar Sanata Gaidam.

Ya ce, “A matsayinmu na al’ummar mazabar Zone A suna alfahari da irin yadda Sanata Gaidam yake kokari wajen jawo hankalin gwamnatin tarayya domin inganta rayuwar yankunan da ke kan iyakar Nijeriya da makobciyarta Nijar. Wanda ko shakka babu hakan zai taimaka wajen farfado da yankunan.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
Siyasa

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Gaidam
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Next Post
Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.