ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

by Muhammad Maitela
4 years ago
Gaidam

Tsohon Gwamnan jihar Yobe, kuma Sanata mai wakiltar shiyya ta daya (Zone A) a zauren majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ibrahim Gaidam tare da hadin gwiwa da Hukumar bunkasa yankunan kan iyakoki ta kasa: Border Communities Development Agency (BCDA)- sun kaddamar da tallafin kayan kiwon Kifi da sana’o’in dogaro da Kai ga matasa da mata sama da 400.

Da ya ke kaddamar da raba tallafin babban dakin taron karamar hukumar Damaturu, a babban birnin jihar Yobe, ranar Asabar, Sanata Gaidam wanda Muhammad Kiwata ya wakilta ya ce wannan kokari domin tallafa wa al’ummar mazaba da kayan sana’o’i hadi da horar da mata da Matasa, suna daga cikin abubuwan da Sanata Gaidam ke yi don kawar da zaman kashe wando domin samar da sana’a don jama’a su dogara da kansu.

  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

Gaidam ya ce ya zama wajibi a matsayin su na shugabannin al’umma su tashi tsaye wajen samarwa da mata da matasa ayyukan yi musamman sana’o’in dogaro da kai, bayar da horo tare da tallafa musu da abubuwan da za su fara sana’o’in a lokacin da suka kammala samun horon.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Saboda haka ne, ta hanyar hadin gwiwar fadar shugaban kasa mu ka yi kokarin bayar da tallafin wadannan kayan fara sana’o’i ga matasanmu sama da 400; domin kiwon Kifi wanda hakan zai taimaka su tsaya da kafafunsu.”

A nashi bangaren, babban jami’in Hukumar BCDA, Mista Rotimi Taiwo ya bukaci matasan su yi amfani da kayan da aka raba musu ta hanyar da ta dace, tare da sanar dasu cewa jami’an hukumar zasu biyo sawu domin tabbatar da cewa matasan basu sayar da kayan ba. Ya yi barazanar mika duk wanda aka kama da sauya akalar kayan zuwa hukumar EEFC.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Wakilinmu ya zanta da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daga karamar hukumar Yunusari, Fusama Alhaji Bai inda ya bayyana cewa, sun yaba matuka dangane da wannan tallafin da suka samu na gwamnatin Tarayya ta hanyar Sanata Gaidam.

Ya ce, “A matsayinmu na al’ummar mazabar Zone A suna alfahari da irin yadda Sanata Gaidam yake kokari wajen jawo hankalin gwamnatin tarayya domin inganta rayuwar yankunan da ke kan iyakar Nijeriya da makobciyarta Nijar. Wanda ko shakka babu hakan zai taimaka wajen farfado da yankunan.” In ji shi.

Gaidam
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.