ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

by Muhammad Maitela
4 years ago
Gaidam

Tsohon Gwamnan jihar Yobe, kuma Sanata mai wakiltar shiyya ta daya (Zone A) a zauren majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ibrahim Gaidam tare da hadin gwiwa da Hukumar bunkasa yankunan kan iyakoki ta kasa: Border Communities Development Agency (BCDA)- sun kaddamar da tallafin kayan kiwon Kifi da sana’o’in dogaro da Kai ga matasa da mata sama da 400.

Da ya ke kaddamar da raba tallafin babban dakin taron karamar hukumar Damaturu, a babban birnin jihar Yobe, ranar Asabar, Sanata Gaidam wanda Muhammad Kiwata ya wakilta ya ce wannan kokari domin tallafa wa al’ummar mazaba da kayan sana’o’i hadi da horar da mata da Matasa, suna daga cikin abubuwan da Sanata Gaidam ke yi don kawar da zaman kashe wando domin samar da sana’a don jama’a su dogara da kansu.

  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

Gaidam ya ce ya zama wajibi a matsayin su na shugabannin al’umma su tashi tsaye wajen samarwa da mata da matasa ayyukan yi musamman sana’o’in dogaro da kai, bayar da horo tare da tallafa musu da abubuwan da za su fara sana’o’in a lokacin da suka kammala samun horon.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Saboda haka ne, ta hanyar hadin gwiwar fadar shugaban kasa mu ka yi kokarin bayar da tallafin wadannan kayan fara sana’o’i ga matasanmu sama da 400; domin kiwon Kifi wanda hakan zai taimaka su tsaya da kafafunsu.”

A nashi bangaren, babban jami’in Hukumar BCDA, Mista Rotimi Taiwo ya bukaci matasan su yi amfani da kayan da aka raba musu ta hanyar da ta dace, tare da sanar dasu cewa jami’an hukumar zasu biyo sawu domin tabbatar da cewa matasan basu sayar da kayan ba. Ya yi barazanar mika duk wanda aka kama da sauya akalar kayan zuwa hukumar EEFC.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Wakilinmu ya zanta da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daga karamar hukumar Yunusari, Fusama Alhaji Bai inda ya bayyana cewa, sun yaba matuka dangane da wannan tallafin da suka samu na gwamnatin Tarayya ta hanyar Sanata Gaidam.

Ya ce, “A matsayinmu na al’ummar mazabar Zone A suna alfahari da irin yadda Sanata Gaidam yake kokari wajen jawo hankalin gwamnatin tarayya domin inganta rayuwar yankunan da ke kan iyakar Nijeriya da makobciyarta Nijar. Wanda ko shakka babu hakan zai taimaka wajen farfado da yankunan.” In ji shi.

Gaidam
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Gaidam
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.