ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

by Sadiq
4 years ago
Machina

Tsohon dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a Jihar Yobe, Abubakar Abubakar Jinjiri, ya janye karar da ya shigar a kan dan takarar kujerar sanata na jam’iyyar APC, Bashir Sheriff Machina da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kuma jam’iyyar APC. 

Sanata Jinjiri, ta bakin lauyansa, Barista Usman Lukman Nuhu, ya shaida wa mai shari’a Fadima Aminu ta babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, cewa an shigar da sanarwar dakatar da wadanda ake kara a kan lamarin.

  • Gobara Ta Tashi A Wani Gidan Man Sayar Da Gas A Fatakwal 
  • Karancin Man Fetur: NSCDC Ta Gargadi Gidajen Mai Kan Boye Man Fetur

LEADERSHIP ta tattaro cewa lamarin ya faru ne jim kadan bayan da aka bukaci a saurari karar a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Barista Nuhu ya sanar da cewar Jinjiri da ya janye karar sannan ya roki kotu da ta dakatar da shari’ar tare da bayar da umarnin soke karar.

Lauyan Machina, Barista Mohammed Ngumurumi wanda ya rike da takaitaccen bayanin Ibrahim Bawa, SAN, ya roki kotun da ta yi watsi da karar maimakon ta soke ta.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Sauran wadanda ake tuhuma kuma ba su yi adawa da sanarwar janye mai karar ba.

A hukuncin da ta yanke, mai shari’a Fadima Aminu ta bayyana cewa Jinjiri na da damar shigar da sanarwar janyewar kararsa.

Ta ce sanarwar dakatarwar ta na nan daram saboda haka ta yi watsi da karar kamar yadda lauyan Machina ya bukata.

A ranar 17 ga watan Yuni ne Jinjiri ya garzaya babbar kotun tarayya da ke Damaturu tare da gabatar da karar gabanin zabe yana kalubalantar takarar Bashir Machina wanda ya lashe zaben fidda gwanin dan takarar Sanata na jam’iyyar APC na mazabar Yobe ta Arewa a ranar 2 ga watan Mayu.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a makonnin da suka gabata ne kotun ta ayyana Machina a matsayin wanda ya cancanta a matsayin zababben dan takarar kujerar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben 2023, wanda hakan ya kawo karshen cece-kuce da suka dabaibaye jam’iyyar APC a Yobe ta Arewa.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.