• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

by Sadiq
1 year ago
Sanusi

Muhammadu Sanusi II, ya bari garin Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas a gaggauce, jim kadan bayan ya gabatar da jawabinsa a babban taron tattalin arziki da zuba jari a jihar.

Sanusi yana tsakiyar gabatar da jawabinsa ne, ‘labarin LEADERSHIP’ na sake nada shi a matsayin Sarkin Kano, ya karade gari.

  • Da Ɗumi-Ɗumi: An Sake Naɗa Sanusi Lamido Sanusi A Matsayin Sarkin Kano
  • Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

LEADERSHIP, ta bayyana cewar, an tsaurara tsaro a tattare da Sanusi lokacin da yake barin wajen taron da ke gudana a Obi Wali International Conference Center a Fatakwal, wanda hakan ya sa ‘yan jarida ba su samu damar tattaunawa da shi ba.

A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya taya Sanusi II murnar sake zama Sarkin Kano.

Fubara, a wata sanarwa da ya fitar a Fatakwal, ya ce ya samu labarin sake nada tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), a matsayin Sarkin Kano, wanda hakan ya sanya shi farin ciki matuka.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Gwamnan, ya kara da cewa sake nada shi sarautar da gwamnatin jihar ta yi, ya nuna cewa tsige Muhammadu Sanusi II da aka yi a ranar 9 ga watan Maris, 2020, bai yi wa al’ummar Jihar Kano dadi ba, wanda ya ce rashin adalci ne ga miliyoyin al’ummar jihar.

Ya yaba wa gwamnatin Jihar Kano bisa yadda ta saurari bukatun jama’a, tare da yin gyara kan abin da aka yi a baya, sannan ya bukaci jama’a da su bai wa Sarkin goyon baya domin samun nasara.

Fubara, ya kuma bukaci shugaban darikar Tijjanniya na Nijeriya, Muhammad Sanusi II da ya jagoranci mabiya darikar sama da miliyan 50 a Nijeriya cikin hikima da jajircewa tare da samar da zaman lafiya da adalci a tsakanin kowa a Kano.

Ya kuma yi wa Sarkin Kano na 14 fatan samun nasara tare da samar da ci gaba ga al’ummar jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Rizhao Dake Lardin Shandong

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Rizhao Dake Lardin Shandong

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.