• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sare Itatuwa Ne Silar Yaduwar Kananan Cututtuka A Tsakanin Al’umma – Jami’in Gandun Daji

by Shehu Yahaya and Sulaiman
1 year ago
itatuwa

Shugaban masu kula da gandun daji a Jihar Kaduna, Jafar Idris Muhammad, ya bayyana cewa yawaitar sare-saren itatuwa su ne silar yaduwar kananan cututtuka da suke addabar al’ummar.

Shugaban ya ce muddin al’umma suka ci gaba da sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, babu shakka sun kulla kawance da kananan cututtuka. Ya ce itatuwa suna taka rawar gani wajen kare garkuwar jikin Dan’adam.

  • An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara
  • Manufar “Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko” Za Ta Samar Da Ci Gaban Da Duniya Ke Muradi

Ya bayyana haka ne a wata zantawa da yayi da wakilinmu a Kaduna, inda ya ce tuni gwamnatin Jihar Kaduna ta fara daukar matakan hukunta masu sare itatuwa ba bisa ka’ida ba.

“Akwai itatuwa masu daraja wadanda sare su babbar illa ce, kamar irinsu dorawa, ka ga dorawa sarata laifi ne babba, wanda ida aka kama mai sare ta sai ya biyu ha-raji na 600,000 ko shekara uku a gidan gyaran hali.

“Yanzu ni idan na samu kuna a jikina, ganyen dorawa nake samowa na kona na shafa a wurin kunan. Cikin kwana biyu zuwa uku zan warke ba tare da na je na sha maganin asibiti ba. Haka kuma akwai itatuwa da suke da amfani ga lafiyar mu-tane amma sai ka ga ana sare su.

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

“Dokar gandun daji ta shekarar 2019 wacce aka sabunta, ta ce idan ka dasa itace a gidanka ka kula da ita har ta girma, ta zama mallakar gandun daji, ba ka da da-mar sare ta sai ka nemi izinin gandun daji saboda ita ma tana da hakki da ‘yanci kamar mutane.

“Lokacin da nake aiki a dajin Birnin Gwari, na kai mutane da yawa gidan yari bisa sarar itace ba bisa ka’ida ba.

“Baya ga illa ga lafiyar Dan’adam, sare itatuwa yana haifar da zaizaiyar kasa, wanda haka ya sa muke fada wa mutane idan ka sare bishiya guda daya, to ka da-sa guda biyar. Burinmu shi ne mu ga ana dasa itatuwa a Jihar Kaduna, ” in ji shi.

Shugaban masu kula da gandun dajin, ya bukaci kungiyoyin masu sarrafa katako da masu sayar da itacen girgi da ‘yan gawayi da su guji sare itatuwan daji ba bisa ka’ida ba.

A cewarsa, akwai itatuwan da hukumar gandun daji take bayar da damar a sare su bisa sharuddan dokar da ta kafa dangun daji. Ya ce duk wanda jami’ansu suka kama yana sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, zai fuskanci fushin hukuma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

October 31, 2025
Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
Manyan Labarai

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

October 31, 2025
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

October 31, 2025
Next Post
sin

Xi Jinping: Inganta Gina Dunkulewar Kabilun Kasar Sin Baki Daya

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

October 31, 2025
Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

October 31, 2025
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

October 31, 2025
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.