ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar “Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko” Za Ta Samar Da Ci Gaban Da Duniya Ke Muradi

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Hajoji

Wata kididdiga da aka fitar yau Talata, ta nuna cewa, adadin kamfanonin dake bangaren sarrafawa da kere-keren kayayyaki a kasar Sin ya kai miliyan 6.03, karuwar kaso 5.53 daga karshen shekarar da ta gabata. 

 

A farkon bara ce kasar Sin ta kaddamar da manufar “sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko” da nufin zama mai dogaro da kanta a bangaren kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da samar da hajoji masu inganci tare da daukaka ayyukan masana’antu.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Tana Raba “Sirrin” Ci Gabanta Ga Afirka
  • Ambaliya: Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Bai Wa Maiduguri Tallafin Miliyan 20

Kasar Sin ba ta fada, ta gaza cikawa. A kullum na kan yi mamakin yadda idan Sin ta furta abu, to sai ta kai ga cimma shi. Kuma na fahimci cewa hakan ba ya rasa nasaba da kyawawan kudurorin gwamnati, ta hanyar daukar ingantattun matakai da goyon bayan da al’umma ke ba ta da kuma kishin kasa dake akwai a zukatan dukkan bangarorin.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Har kullum, gwamnati da al’ummar kasar Sin ba sa duba moriyarsu ta kashin kai, sai yadda kasar baki daya za ta amfana. Shi ya sa idan gwamnatin kasar Sin ta gabatar da wata manufa ko burin da take son cimmawa, to al’ummarta za su yi na’am su karba da hannu bibbiyu domin bayar da gudunmuwarsu wajen cimma wannan buri.

 

Karuwar adadin kamfanonin da aka samu a bana, ya kara tabbatar da cewa, burin kasar Sin na zama mai dogaro da kanta na gab da cika. Wannan labari ne mai dadi ba ga kasar Sin kadai ba, har ma da sauran kasashe abokan huldarta, musammam masu tasowa, domin ci gaban kasar Sin, ci gaban su ne da duk sauran sassan duniya. Kana hakan zai kyautata wadatar kayayyakin da ake bukata da za su kasance masu inganci da rahusa ba tare da fuskantar tangarda ko kariyar cinikayya ba.

 

Yayin da wasu kasashe suka nace ga kariyar cinikayya, wannan manufa ta kasar Sin, za ta habaka tsarin harkokin cinikayya a duniya, haka kuma za ta bunkasa tsarin samar da kayayyaki ta yadda abubuwan da ake bukata a duniya za su wadatu. Haka kuma, kasar Sin za ta zama jagora wajen ganin dunkulewar duniya da inganta dangantakar cinikayya tsakanin sassa daban daban, wanda zai kara kawo cudanyar mabanbantan al’ummu da fahimtar juna da wanzuwar zaman lafiya da samar da al’umma mai makoma ta bai daya, wato dai, ci gaban da ake fata.

 

Bugu da kari, zai kara bayyana illolin kariyar cinikayya da wasu kasashe ke aiwatarwa, domin yunkurinsu na mayar da Sin saniyar ware ba zai yi nasara ba, sai dai su ware kansu daga ci gaban da duniya za ta samu ta kuma mora.

Hajoji
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Hajoji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Tsohon Kwamishinan Tambuwal Ya Musanta Zargin Hannun Jarin Biliyan 16

Tsohon Kwamishinan Tambuwal Ya Musanta Zargin Hannun Jarin Biliyan 16

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.