Allah Ya yi wa Sarkin Tikau a Jihar Yobe, Alhaji Muhammadu Abubakar Ibn Grema ya rasuwa.
Wata majiya daga iyalinsa ce ta tabbatar da rasuwar Sarkin da yammacin ranar Juma’a, bayan ya sha fama da doguwar jinya a Asibitin Kwararru na Potiskum.
- PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya
- ‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara
Ya rasu ya bar mata uku da ’ya’ya da jikoki da dama.
Talla
Marafan Tikau, Alhaji Shaibu Baba Alaraba, ya mika ta’aziyyarsa game da rasuwar sarkin.
Ya bayyana marigayi Sarkin a matsayin “Shugaba nagari kuma mutum mai kima a cikin al’umma, wanda ya kware wajen nuna tausayi, hikima da sadaukar da kai domin jin dadin al’ummarsa.
Talla