ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PRP

Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen gargadin gwamnatin tarayya kan gayyato sojojin Amurka da wasu sauran kasashen Turai domin su kafa sansanoninsu na soja a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar tare da sa hannun mukaddashin sakataren yada labaranta na kasa, Kwamared Muhammed Ishak, ta ce barin sojojin kasashen waje su shigo Nijeriya bayan an kore su daga wasu kasashe kamar irinsu Senegal da Nigarr babban hatsari ne ga tsaron kasa da kuma lafiyar ‘yan Nijeriya.

  • CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya 
  • Sinawa Ba Za Su Manta Da Danyen Laifin NATO Na Kai Wa Yugoslavia Hari Ba

Jam’iyyar ta bukaci gwamnatin tarayya ta yi watsi da irin wannnan tunani domin bai dace da manufar kasa ba, saboda baraza ce ga ‘yancin Nijeriya da tattalin arziki da difilomasiyya na tusa manufar kasashen waje cikin kasa mai ‘yancin gashin kai kamar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen jawo hankalin Shugaban kasa, Bola Tinubu da majalisar kasa kan illar gayyato sojojin Amurka da wasu kasashen Turai na kafa sassanin soja a Nijeriya, bayan da aka fatattake su daga wasu kasashe.

“Matsayar jam’iyyar PRP kan wannan yunkurin dai shi ne, akwai matukar illa ga sha’anin tsaron kasarmu da ‘yancin gashin kai. Domin haka ne muke gargadin gwamnatin Nijeriya ba ma goyon bayan wannan lamari.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Gayyato wadannan sojoji zuwa kasarmu domin su kafa sassani ba karamin illa ba ce ga harkokin tsaronmu da kuma lafiyar ‘yan ksarmu. Bisa tsarin da aka kafa jam’iyyarmu na samun cikakken ‘yanci, wannan ya saba da ra’ayin kasarmu saboda dalilai da dama.

“Shigowar sojojin zai kara tauye ‘yancinmu wajen shigo da ra’ayoyin ‘yan kasashen ketare a kasarmu ta gado. Sannan za a samu sabon barazana kan harkokin tsaro, domin wadannan sojojin ba su san sha’anin tsaron Nijeriya ba wanda haka ka iya janyo hatsarin ta’addanci da sauran rikice-rikice.

“Dole ne gwamnatin Nijeriya ta yi la’akari da illar da wannan lamari zai yi wa tattalin arziki idan hharr sojojin kasashen waje suka kafa sassaninsu a Nijeriya. Za a samu tsadar masaukin sojojin da kulawa da ababen more rayuwarsu. Bugu da kari, akwai babban illa wajenn kulawa da sojojin kasashen ketare.”

Sai dai kuma, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris Malagi, ya musanta cewa Nijeriya na shirin amincewa a kafa sansanonin sojin na kasashen waje a kasarta, yana mai cewar masu yamadidi ne kawai suka kitsa maganar kuma suke ta yadawa.

“Ina mai tabbatar wa da ‘yan kasa cewa babu wannan shirin. Akwai kasashen da muke kawance da su don yaki da matsalar tsaronmu, wannan muna ci gaba da yi, amma ba wai batun kafa sansanonin sojojinsu. Jita-jita ce kawai!”.

PRP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.