• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

by Sadiq
3 years ago
Saudiyya

Kasashen Larabawa na yankin Gulf sun nemi kamfanin Netflix ya cire dukkan fina-finan da suka sabawa dokokin Musulunci da al’adun tarbiyya, kamar yadda kafar yada labarai ta Saudiyya ta ruwaito.

A wata sanarwa da kungiyar kasashen yankin Gulf ta fitar ta yi gargadi cewar wasu fina-finai na baya-bayan nan da aka yi don yara sun saba wa dokokin musulunci.

  • Lauyoyi Sun Maka Ado Gwanja, Safara’u, 442 Da Wasu ‘Yan TikTok A Kotu
  • Buhari Ya Kaddamar Da Wani Kwamiti Da Zai Sake Duba Bukatun Kungiyar ASUU

Kafar talabijin ta Saudiyya ta nuna wasu bidiyo da aka dusaseh fuskarsu na katun din fim din Jurassic World: Camp Cretaceous, wanda aka nuna wasu yara mata biyu suka nuna suna son juna tare da sumbatar juna.

Gidan talabijin na Al Ekhbariya da ya nuna wani sashe na fim din da wani kamfanin Faransa na Cuties ya shirya, ya sanya take kamar haka “bidiyon da ke nuna rashin da’a da rusa tarbiyya wanda ke barazanar lalata tarbiyyar yara.”

A wani bidiyon da Al Ekhbariya ta wallafa a shafinta na Intanet, ta yi zargin cewa fim din na “yada luwadi da madigo ne.”

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Hakazalika gidan talabijin din ya yi hira da mutane da dama da suka yi irin wanan zargin tare da kiran hukumomi su dauki mataki cikin gaggawa.

An tuntubi Netflix da ya cire bidiyon, da kuma duk wasu fina-finai da aka shirya don yara, tare da tabbatar da bin dokoki,” kamar yadda sanarwar hadin gwiwa daga hukumar kula da fina-finai ta Saudiyya da ta kula da kafafen yada labarai.

Hukumomi za su sa ido don ganin ko an bi umarnin, tare da daukar matakan shari’a idan har aka ci gaba da yada fina-finan”, kamar yadda suka yi gargadin.

Babu wani martani daga kamfanin Netflix, duk da cewa Saudiyya ba ta da wasu dokoki na damar zabar jinsi, amma yin luwadi da madigo da zina haramun ne a kasar.

A karkashin dokokin Musulunci na kasar dai, hukuncin duk wanda aka kama da laifin luwadi ko madigo hukuncin kisa ne ko bulala, ya dangata girman laifin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
Ana Zargin Budurwa Da Kashe Mahaifiyar Saurayinta Da Adda A Kamaru

Ana Zargin Budurwa Da Kashe Mahaifiyar Saurayinta Da Adda A Kamaru

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.