• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

by Abdulmumin Murtala
1 year ago
in Labarai
0
Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Saudiyya, ta hannun babban jami’in Jakadancinta da ke Jihar Kano, ta ba da gudunmawar dabino ga Masallatan Juma’a, makarantun islamiyya, gidajen marayu da asibitoci a jihar. 

Katan 3000 ne na dabino gwamnatin Jihar Kano ta karba a ranar Laraba, wanda sakataren gwamnatin jihar, Baffa Bichi ya wakilci gwamna Abba Kabir Yusuf.

  • PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200
  • Matatar Dangote Ta Sake Karya Farashin Dizal Da Man Jirgi

A lokacin da Bichi ke karbar dabinon a madadin wadanda aka bai wa, ya bayyana farin cikin gwamnatin Kano da irin gudunmawar da ta ke samu daga Saudiyya.

“Muna godiya ga Allah da irin wannan taimako da gudunmawa da muke samu daga jama’a da gwamnatin Saudiyya.

“Za mu tabbatar cewa wannan dabino da aka raba sun iske wadanda aka yi domin su. Za a yi rabon dabinon kamar yadda aka tsara a rubuce” in ji Bichi.

Labarai Masu Nasaba

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yayin da yake mika dabinon, babban Jami’in Jakadancin Saudiyya da ke Kano, Khaleel Ahmad Adamawiy, ya ba da tabbacin cewa gwamnatin Saudiyya ta karkashin hukumar ba da taimako da tallafin gaggawa na masarautar kasar, na ba da taimako da yawa a Nijeriya a bangarori da dama.

“Nan kusa a cikin shekarar da ta gabata, mun gabatar da tsarin ciyarwa da mutane 48,300 suka amfana da kayan tallafin abincin a Jihar Kano da Yobe da kuma Borno inda aka kashe Dala 500,000.

“Haka kuma a Kano an ciyar da kimanin iyalai 2,056 a wannan shekarar.

“Hukumar ta gabatar da ayyukan kula da lafiya a Abuja da Legas a cikin manufarta na ba da taimako ga mabukata da kuma tsarinta na taimaka wa masu rauni domin rage musu radadin talauci.

“Wannan gudunmawa na dabino na daga cikin irin wadannan ayyuka da ake gabatarwa da sahalewar mai kula da Masallatan biyu masu tsarki, zuwa ga kasashe da ake aminci da su da suka hada da Nijeriya, domin tabbatarwa da an taimaka wa iyalai masu bukata a fadin duniya” in ji Adamawiy.

A cikin jawabinsa ya bayyana cewa kafa wannan hukumar bayar da taimako da tallafin gaggawa ta Sarki Salman a ranar 15 ga watan Mayu, 2015, tare da taimakon kasashe 175 na Majalisar Dinkin Duniya, hukumar ta kammala ayyuka da ba da taimako da aka kiyasta kudinsu ya kai dala biliyan 6.2 a kasashe 91.

Tuni gwamnatin Jihar Kano ta fara raba dabinon ga wadanda aka bayar dominsu a Jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabinokanoSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ta’addanci Na Haifar Da Illa Musamman Ga Mata — Amina Mohammed

Next Post

Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

Related

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

5 minutes ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

3 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

4 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

12 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

15 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

18 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.