• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

by Abdulmumin Murtala
1 year ago
in Labarai
0
Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Saudiyya, ta hannun babban jami’in Jakadancinta da ke Jihar Kano, ta ba da gudunmawar dabino ga Masallatan Juma’a, makarantun islamiyya, gidajen marayu da asibitoci a jihar. 

Katan 3000 ne na dabino gwamnatin Jihar Kano ta karba a ranar Laraba, wanda sakataren gwamnatin jihar, Baffa Bichi ya wakilci gwamna Abba Kabir Yusuf.

  • PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200
  • Matatar Dangote Ta Sake Karya Farashin Dizal Da Man Jirgi

A lokacin da Bichi ke karbar dabinon a madadin wadanda aka bai wa, ya bayyana farin cikin gwamnatin Kano da irin gudunmawar da ta ke samu daga Saudiyya.

“Muna godiya ga Allah da irin wannan taimako da gudunmawa da muke samu daga jama’a da gwamnatin Saudiyya.

“Za mu tabbatar cewa wannan dabino da aka raba sun iske wadanda aka yi domin su. Za a yi rabon dabinon kamar yadda aka tsara a rubuce” in ji Bichi.

Labarai Masu Nasaba

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Yayin da yake mika dabinon, babban Jami’in Jakadancin Saudiyya da ke Kano, Khaleel Ahmad Adamawiy, ya ba da tabbacin cewa gwamnatin Saudiyya ta karkashin hukumar ba da taimako da tallafin gaggawa na masarautar kasar, na ba da taimako da yawa a Nijeriya a bangarori da dama.

“Nan kusa a cikin shekarar da ta gabata, mun gabatar da tsarin ciyarwa da mutane 48,300 suka amfana da kayan tallafin abincin a Jihar Kano da Yobe da kuma Borno inda aka kashe Dala 500,000.

“Haka kuma a Kano an ciyar da kimanin iyalai 2,056 a wannan shekarar.

“Hukumar ta gabatar da ayyukan kula da lafiya a Abuja da Legas a cikin manufarta na ba da taimako ga mabukata da kuma tsarinta na taimaka wa masu rauni domin rage musu radadin talauci.

“Wannan gudunmawa na dabino na daga cikin irin wadannan ayyuka da ake gabatarwa da sahalewar mai kula da Masallatan biyu masu tsarki, zuwa ga kasashe da ake aminci da su da suka hada da Nijeriya, domin tabbatarwa da an taimaka wa iyalai masu bukata a fadin duniya” in ji Adamawiy.

A cikin jawabinsa ya bayyana cewa kafa wannan hukumar bayar da taimako da tallafin gaggawa ta Sarki Salman a ranar 15 ga watan Mayu, 2015, tare da taimakon kasashe 175 na Majalisar Dinkin Duniya, hukumar ta kammala ayyuka da ba da taimako da aka kiyasta kudinsu ya kai dala biliyan 6.2 a kasashe 91.

Tuni gwamnatin Jihar Kano ta fara raba dabinon ga wadanda aka bayar dominsu a Jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabinokanoSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ta’addanci Na Haifar Da Illa Musamman Ga Mata — Amina Mohammed

Next Post

Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

Related

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

3 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

4 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

5 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

6 hours ago
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
Labarai

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

8 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.