ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

by Abdulmumin Murtala
2 years ago
Dabino

Gwamnatin Saudiyya, ta hannun babban jami’in Jakadancinta da ke Jihar Kano, ta ba da gudunmawar dabino ga Masallatan Juma’a, makarantun islamiyya, gidajen marayu da asibitoci a jihar. 

Katan 3000 ne na dabino gwamnatin Jihar Kano ta karba a ranar Laraba, wanda sakataren gwamnatin jihar, Baffa Bichi ya wakilci gwamna Abba Kabir Yusuf.

  • PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200
  • Matatar Dangote Ta Sake Karya Farashin Dizal Da Man Jirgi

A lokacin da Bichi ke karbar dabinon a madadin wadanda aka bai wa, ya bayyana farin cikin gwamnatin Kano da irin gudunmawar da ta ke samu daga Saudiyya.

ADVERTISEMENT

“Muna godiya ga Allah da irin wannan taimako da gudunmawa da muke samu daga jama’a da gwamnatin Saudiyya.

“Za mu tabbatar cewa wannan dabino da aka raba sun iske wadanda aka yi domin su. Za a yi rabon dabinon kamar yadda aka tsara a rubuce” in ji Bichi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yayin da yake mika dabinon, babban Jami’in Jakadancin Saudiyya da ke Kano, Khaleel Ahmad Adamawiy, ya ba da tabbacin cewa gwamnatin Saudiyya ta karkashin hukumar ba da taimako da tallafin gaggawa na masarautar kasar, na ba da taimako da yawa a Nijeriya a bangarori da dama.

“Nan kusa a cikin shekarar da ta gabata, mun gabatar da tsarin ciyarwa da mutane 48,300 suka amfana da kayan tallafin abincin a Jihar Kano da Yobe da kuma Borno inda aka kashe Dala 500,000.

“Haka kuma a Kano an ciyar da kimanin iyalai 2,056 a wannan shekarar.

“Hukumar ta gabatar da ayyukan kula da lafiya a Abuja da Legas a cikin manufarta na ba da taimako ga mabukata da kuma tsarinta na taimaka wa masu rauni domin rage musu radadin talauci.

“Wannan gudunmawa na dabino na daga cikin irin wadannan ayyuka da ake gabatarwa da sahalewar mai kula da Masallatan biyu masu tsarki, zuwa ga kasashe da ake aminci da su da suka hada da Nijeriya, domin tabbatarwa da an taimaka wa iyalai masu bukata a fadin duniya” in ji Adamawiy.

A cikin jawabinsa ya bayyana cewa kafa wannan hukumar bayar da taimako da tallafin gaggawa ta Sarki Salman a ranar 15 ga watan Mayu, 2015, tare da taimakon kasashe 175 na Majalisar Dinkin Duniya, hukumar ta kammala ayyuka da ba da taimako da aka kiyasta kudinsu ya kai dala biliyan 6.2 a kasashe 91.

Tuni gwamnatin Jihar Kano ta fara raba dabinon ga wadanda aka bayar dominsu a Jihar.

Dabino
Abdulmumin Murtala
+ postsBio
  • Abdulmumin Murtala
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulmumin-murtala/
    Hisba Ta Cafke Mata 7 Da Ake Zargi Da Satar Yadidduka A Kano

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.