ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Raba Dabino Ga Makarantu, Gidajen Marayu Da Asibitoci A Kano

by Abdulmumin Murtala
2 years ago
Dabino

Gwamnatin Saudiyya, ta hannun babban jami’in Jakadancinta da ke Jihar Kano, ta ba da gudunmawar dabino ga Masallatan Juma’a, makarantun islamiyya, gidajen marayu da asibitoci a jihar. 

Katan 3000 ne na dabino gwamnatin Jihar Kano ta karba a ranar Laraba, wanda sakataren gwamnatin jihar, Baffa Bichi ya wakilci gwamna Abba Kabir Yusuf.

  • PSG Na Neman Dauko Lamine Yamal Daga Barcelona A Kan Yuro Miliyan 200
  • Matatar Dangote Ta Sake Karya Farashin Dizal Da Man Jirgi

A lokacin da Bichi ke karbar dabinon a madadin wadanda aka bai wa, ya bayyana farin cikin gwamnatin Kano da irin gudunmawar da ta ke samu daga Saudiyya.

ADVERTISEMENT

“Muna godiya ga Allah da irin wannan taimako da gudunmawa da muke samu daga jama’a da gwamnatin Saudiyya.

“Za mu tabbatar cewa wannan dabino da aka raba sun iske wadanda aka yi domin su. Za a yi rabon dabinon kamar yadda aka tsara a rubuce” in ji Bichi.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Yayin da yake mika dabinon, babban Jami’in Jakadancin Saudiyya da ke Kano, Khaleel Ahmad Adamawiy, ya ba da tabbacin cewa gwamnatin Saudiyya ta karkashin hukumar ba da taimako da tallafin gaggawa na masarautar kasar, na ba da taimako da yawa a Nijeriya a bangarori da dama.

“Nan kusa a cikin shekarar da ta gabata, mun gabatar da tsarin ciyarwa da mutane 48,300 suka amfana da kayan tallafin abincin a Jihar Kano da Yobe da kuma Borno inda aka kashe Dala 500,000.

“Haka kuma a Kano an ciyar da kimanin iyalai 2,056 a wannan shekarar.

“Hukumar ta gabatar da ayyukan kula da lafiya a Abuja da Legas a cikin manufarta na ba da taimako ga mabukata da kuma tsarinta na taimaka wa masu rauni domin rage musu radadin talauci.

“Wannan gudunmawa na dabino na daga cikin irin wadannan ayyuka da ake gabatarwa da sahalewar mai kula da Masallatan biyu masu tsarki, zuwa ga kasashe da ake aminci da su da suka hada da Nijeriya, domin tabbatarwa da an taimaka wa iyalai masu bukata a fadin duniya” in ji Adamawiy.

A cikin jawabinsa ya bayyana cewa kafa wannan hukumar bayar da taimako da tallafin gaggawa ta Sarki Salman a ranar 15 ga watan Mayu, 2015, tare da taimakon kasashe 175 na Majalisar Dinkin Duniya, hukumar ta kammala ayyuka da ba da taimako da aka kiyasta kudinsu ya kai dala biliyan 6.2 a kasashe 91.

Tuni gwamnatin Jihar Kano ta fara raba dabinon ga wadanda aka bayar dominsu a Jihar.

Dabino
Abdulmumin Murtala
+ postsBio
  • Abdulmumin Murtala
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulmumin-murtala/
    Hisba Ta Cafke Mata 7 Da Ake Zargi Da Satar Yadidduka A Kano

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

Gwamnan Kano Ya Isa Amurka Domin Taron Tattaunawa Kan Kalubalen Tsaro A Arewacin Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.