• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Kudi: Tunibu Ya Kutsa Kai Wurin Taron Gaggawa Da APC Ta Kira Gwamnoninta A Abuja

by Muhammad
3 years ago
Sauyin Kudi

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki, Bola Tinubu, ya shiga taron gaggawa na gwamnonin jam’iyyar da ke gudana yanzu haka a Abuja.

Ana ci gaba da wani taron gaggawa na gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja.

  • ‘Rikicin Sauya Kudi’: Adamu Da Gwamnonin APC Sun Shiga Taron Gaggawa Na Sirri A Abuja
  • Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ne ya kira taron domin tattauna batutuwan da suka shafi yakin neman zabe, rikicin Naira da kuma zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar Asabar mai zuwa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen sakatariyar yayin da ake ci gaba da gudanar da taron na sirri.

Gwamna Nasir El-Rufai (Kaduna), Abdullahi Sule (Nasarawa), Bello Matawalle (Zamfara) da Simon Lalong (Plateau) da kuma Mai Mala Buni (Yobe) na daga cikin gwamnonin da suka halarci taron.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

A jawabinsa na bude taron, Adamu ya ce, “Na yi farin ciki da amsar da aka bayar kawo yanzu. Kuma ni a fahimtata da yawa daga cikin gwamnonin suna kan hanyarsu ta zuwa. Nasan kuna sane da dalilan da suka wajabta buƙatar wannan gayyata sakamakon yadda lamura suke tafiya a yanzu.

“Ba ma son zama a yanke hukunci ga kowa ko hukumomi game da abin da ke faruwa a kasar a yau kamar yadda lamarin ya shafi babbar jam’iyyarmu.

“Na ga abin da ya fi dacewa a yi shi ne a samu duk masu rike da madafun iko a cikin jam’iyya, mu hadu a yi mu’amala da juna ta yadda za mu iya samun kyakkyawar matsaya don magance yanayin da muke ciki.”

Wasu gwamnonin jam’iyyar APC sun shigar da kara a gaban gwamnatin tarayya kan batun sake fasalin naira.

Kotun koli ta umarci CBN da kada ya aiwatar da wa’adin amma Godwin Emefiele, gwamnan CBN ya ce babu bukatar a canza wa’adin.

Buhari dai ya bi umarnin kotu ta wani bangare bayan da ya bayar da umarnin tsawaita wa’adin Naira 200 tare da bayyana cewa tsofaffin takardun N500 da N1000 a dakatar da karbarsu.

Hakan ya jawo cece-kuce a fadin kasar. Gwamnonin jam’iyya mai mulki sun bi sahun masu sukar Buhari kan lamarin.

Yayin da Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano ya yi zargin cewa manufar sake fasalin Naira na da nufin durkusar da dimokuradiyyar Nijeriya, takwaransa na Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bukaci mazauna yankin da su yi watsi da umarnin Buhari.

Gwamna Dapo Abidoun (Ogun) da Babajide Sanwo-Olu (Lagos), Abubakar Badaru (Jigawa) na daga cikin wadanda suka bayyana cewa har yanzu ana amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 a jihohinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Kwarewar Sin A Fannin Noman Shinkafa Ta Burge Hukumomin Malawi

Kwarewar Sin A Fannin Noman Shinkafa Ta Burge Hukumomin Malawi

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.