• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

by Abubakar Sulaiman
4 months ago
ADC

Yayin da fafutukar neman nasara a zaɓen shekarar 2027 ke ɗaukar zafi, bayan ƙaddamar da shugabancin riƙon ƙwarya na shugabancin jam’iyyar ADC a matakin ƙasa, magoya bayan jam’iyyar PDP da wasu jam’iyyun adawa sun fara komawa sabuwar jam’iyyar adawa ta haɗaka a jihar Borno.

Fitattun ƴan siyasa daga jam’iyyun adawa sun bayyana ADC a makon da ya gabata a matsayin sabon dandalin haɗin gwuiwa don ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Tinubu da jam’iyyarsa ta APC a babban zaɓen 2027.

  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna tsohon ɗan takarar gwamna a PDP kuma jigo a APC, Mattawali Kashim Ibrahim Imam, yana karɓar baƙuncin wasu manyan ƴan siyasa a gidansa da ke Maiduguri, inda aka bayyana cewa sun tattauna batun sauya sheƙa zuwa ADC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa manyan ƴan adawan Nijeriya guda biyu — Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na Labour Party — sun nuna goyon baya ga sabon dandalin siyasa na ADC. Sai dai gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya musanta raɗe-raɗin cewa shi da wasu gwamnoni guda biyar za su fice daga APC zuwa sabuwar jam’iyyar haɗaka.

Rahotannin sun nuna cewa Idris Mamman Durkwa, tsohon ɗan takarar gwamna, da Hon. Sheriff Banki, wani fitaccen matashi mai samun goyon bayan jama’a, sun jagoranci ficewar dubban mambobi daga PDP zuwa ADC.

LABARAI MASU NASABA

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

Sannan kuma akwai Hon. Mohammed Umara Kumalia, tsohon jagoran ƴan adawa a Majalisar Wakilai; Alhaji Saleh Kida, mataimakin ɗan takarar gwamna na PDP a 2023; da Hon. Abdulrazaq Ahmed Zanna, ɗan takarar majalisa daga Bama, Ngala, da Kala Balge, da dama daga cikin tsofaffin ‘yan takara da shugabannin jam’iyyar da suka fice daga PDP da APC.

A cewar Hon. Banki, wannan babban sauyi da ake gani a jihar Borno na nuna gajiya da gazawar gwamnatin APC a matakin ƙasa da jiha. Ya caccaki shugabancin PDP na jihar ƙarƙashin Hon. Zanna Gadama da cewa sun miƙa wuya ga “matsin lamba daga sama,” wanda hakan ya haifar da ficewar mambobi masu yawa. Ya kuma ce tsadar rayuwa da rashin tsaro sun ƙara jefa mutane cikin ƙunci, wanda hakan ya sa jama’a ke neman mafita daga irin wannan jagoranci.

Ya buƙaci jama’ar jihar su marawa ADC baya, yana mai bayyana ta a matsayin jam’iyyar da za ta dawo da dimokuraɗiyya ta gari tare da ceto al’ummar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
Manyan Labarai

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Next Post
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.