• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da fafutukar neman nasara a zaɓen shekarar 2027 ke ɗaukar zafi, bayan ƙaddamar da shugabancin riƙon ƙwarya na shugabancin jam’iyyar ADC a matakin ƙasa, magoya bayan jam’iyyar PDP da wasu jam’iyyun adawa sun fara komawa sabuwar jam’iyyar adawa ta haɗaka a jihar Borno.

Fitattun ƴan siyasa daga jam’iyyun adawa sun bayyana ADC a makon da ya gabata a matsayin sabon dandalin haɗin gwuiwa don ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Tinubu da jam’iyyarsa ta APC a babban zaɓen 2027.

  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna tsohon ɗan takarar gwamna a PDP kuma jigo a APC, Mattawali Kashim Ibrahim Imam, yana karɓar baƙuncin wasu manyan ƴan siyasa a gidansa da ke Maiduguri, inda aka bayyana cewa sun tattauna batun sauya sheƙa zuwa ADC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa manyan ƴan adawan Nijeriya guda biyu — Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na Labour Party — sun nuna goyon baya ga sabon dandalin siyasa na ADC. Sai dai gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya musanta raɗe-raɗin cewa shi da wasu gwamnoni guda biyar za su fice daga APC zuwa sabuwar jam’iyyar haɗaka.

Rahotannin sun nuna cewa Idris Mamman Durkwa, tsohon ɗan takarar gwamna, da Hon. Sheriff Banki, wani fitaccen matashi mai samun goyon bayan jama’a, sun jagoranci ficewar dubban mambobi daga PDP zuwa ADC.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Sannan kuma akwai Hon. Mohammed Umara Kumalia, tsohon jagoran ƴan adawa a Majalisar Wakilai; Alhaji Saleh Kida, mataimakin ɗan takarar gwamna na PDP a 2023; da Hon. Abdulrazaq Ahmed Zanna, ɗan takarar majalisa daga Bama, Ngala, da Kala Balge, da dama daga cikin tsofaffin ‘yan takara da shugabannin jam’iyyar da suka fice daga PDP da APC.

A cewar Hon. Banki, wannan babban sauyi da ake gani a jihar Borno na nuna gajiya da gazawar gwamnatin APC a matakin ƙasa da jiha. Ya caccaki shugabancin PDP na jihar ƙarƙashin Hon. Zanna Gadama da cewa sun miƙa wuya ga “matsin lamba daga sama,” wanda hakan ya haifar da ficewar mambobi masu yawa. Ya kuma ce tsadar rayuwa da rashin tsaro sun ƙara jefa mutane cikin ƙunci, wanda hakan ya sa jama’a ke neman mafita daga irin wannan jagoranci.

Ya buƙaci jama’ar jihar su marawa ADC baya, yana mai bayyana ta a matsayin jam’iyyar da za ta dawo da dimokuraɗiyya ta gari tare da ceto al’ummar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCBornoPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

Next Post

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Related

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

13 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 day ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Next Post
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.