• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da fafutukar neman nasara a zaɓen shekarar 2027 ke ɗaukar zafi, bayan ƙaddamar da shugabancin riƙon ƙwarya na shugabancin jam’iyyar ADC a matakin ƙasa, magoya bayan jam’iyyar PDP da wasu jam’iyyun adawa sun fara komawa sabuwar jam’iyyar adawa ta haɗaka a jihar Borno.

Fitattun ƴan siyasa daga jam’iyyun adawa sun bayyana ADC a makon da ya gabata a matsayin sabon dandalin haɗin gwuiwa don ƙalubalantar shugaban ƙasa Bola Tinubu da jam’iyyarsa ta APC a babban zaɓen 2027.

  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna tsohon ɗan takarar gwamna a PDP kuma jigo a APC, Mattawali Kashim Ibrahim Imam, yana karɓar baƙuncin wasu manyan ƴan siyasa a gidansa da ke Maiduguri, inda aka bayyana cewa sun tattauna batun sauya sheƙa zuwa ADC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa manyan ƴan adawan Nijeriya guda biyu — Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na Labour Party — sun nuna goyon baya ga sabon dandalin siyasa na ADC. Sai dai gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya musanta raɗe-raɗin cewa shi da wasu gwamnoni guda biyar za su fice daga APC zuwa sabuwar jam’iyyar haɗaka.

Rahotannin sun nuna cewa Idris Mamman Durkwa, tsohon ɗan takarar gwamna, da Hon. Sheriff Banki, wani fitaccen matashi mai samun goyon bayan jama’a, sun jagoranci ficewar dubban mambobi daga PDP zuwa ADC.

Labarai Masu Nasaba

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Sannan kuma akwai Hon. Mohammed Umara Kumalia, tsohon jagoran ƴan adawa a Majalisar Wakilai; Alhaji Saleh Kida, mataimakin ɗan takarar gwamna na PDP a 2023; da Hon. Abdulrazaq Ahmed Zanna, ɗan takarar majalisa daga Bama, Ngala, da Kala Balge, da dama daga cikin tsofaffin ‘yan takara da shugabannin jam’iyyar da suka fice daga PDP da APC.

A cewar Hon. Banki, wannan babban sauyi da ake gani a jihar Borno na nuna gajiya da gazawar gwamnatin APC a matakin ƙasa da jiha. Ya caccaki shugabancin PDP na jihar ƙarƙashin Hon. Zanna Gadama da cewa sun miƙa wuya ga “matsin lamba daga sama,” wanda hakan ya haifar da ficewar mambobi masu yawa. Ya kuma ce tsadar rayuwa da rashin tsaro sun ƙara jefa mutane cikin ƙunci, wanda hakan ya sa jama’a ke neman mafita daga irin wannan jagoranci.

Ya buƙaci jama’ar jihar su marawa ADC baya, yana mai bayyana ta a matsayin jam’iyyar da za ta dawo da dimokuraɗiyya ta gari tare da ceto al’ummar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCBornoPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

Next Post

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Related

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

2 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

3 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

17 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

20 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

24 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

1 day ago
Next Post
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.