• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan kotun koli ta tabbatar da nasarar zaben Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban Nijeriya, yanzu lokaci ya yi da shugaban kasar zai mayar da hankali wajen inganta gwamnatinsa ta yadda zai iya tunkarar matsaloli da ke fuskantar Nijeriya kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe.

Kwanaki sama da 50 kenan da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta goyi bayan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a kan ayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu shi ya yi nasara a zaben da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023. Yayin da ita ma kotun koli a ranar Alhamis, 26 ga Oktoba ta tabbatar da wannan hukunci.

  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi

A hukuncin, alkalan kotun kolin su bakwai sun bayyana cewa wadanda suka shigar da kara sun gaza kawo kararan hujjoji da za su kore nasarar da Tinubu ya samu a zaben shugaban kasar.

Bayan watsi da kararrakin guda biyu da ‘yan takarar jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar da na LP, Mista Peter Obi suka shigar, kotun kolin ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta yanke a ranar 6 ga watan Satumba, inda ta tabbatar da ayyana Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya.

Hukuncin da kotun koli ta yanke, ba wai kawai ya kawo karshen duk wasu kararraki da suka shafi zaben shugaban kasa ba, har ma da tabbatar da aikin shugaban kasa na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ayyukan sun hada da samar da ingantacciyar shugabanci, samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya wanda hakan ta sa aka cire tallafin man fetur da kuma dawo da darajar naira, wanda gwamnatin Tinubu ta fara tun daga farkon lamari.

Sai dai babban kalubalen da ke fuskantar ‘yan Nijeriya sun hada da rashin zaman lafiya, rashin samun ci gaba, ayyukan ‘yan bindiga da kuma cin hanci da rashawa.

Kamar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke cewa, “idan ba mu yaki ci hanci da rashawa ba, to zai kashe mu “. Cin hanci da rashawa kamar wutar daji ce da ke cin zukatan ‘yan Nijeriya. Babu wani bangare na rayuwar ‘yan Nijeriya da cin hanci bai dabaibaye ba.

Domin haka, dole ne gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen karfafa yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin yakin neman zabe, Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin sake farfado da darajar Nijeriya.

Lallai idan har ‘yan Nijeriya za su ga sauyi, to dole ne Tinubu ya tashi tsaye wajen inganta gwamnatinsa da kuma yaki da cin hanci da rashawa a kowani bangare. Mafi yawancin mutane sun yi kara ga shugaban kasa ya yi kokarin gudanar da shugabanci nagari ta yadda zai iya farfado da darajar Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau

Next Post

Tsaro: Bai Wa Al’umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 day ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 days ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

1 week ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

1 week ago
Next Post
Tsaro: Bai Wa Al’umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

Tsaro: Bai Wa Al'umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.