ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Sharhi

Bayan kotun koli ta tabbatar da nasarar zaben Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban Nijeriya, yanzu lokaci ya yi da shugaban kasar zai mayar da hankali wajen inganta gwamnatinsa ta yadda zai iya tunkarar matsaloli da ke fuskantar Nijeriya kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe.

Kwanaki sama da 50 kenan da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta goyi bayan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a kan ayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu shi ya yi nasara a zaben da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023. Yayin da ita ma kotun koli a ranar Alhamis, 26 ga Oktoba ta tabbatar da wannan hukunci.

  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi

A hukuncin, alkalan kotun kolin su bakwai sun bayyana cewa wadanda suka shigar da kara sun gaza kawo kararan hujjoji da za su kore nasarar da Tinubu ya samu a zaben shugaban kasar.

ADVERTISEMENT

Bayan watsi da kararrakin guda biyu da ‘yan takarar jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar da na LP, Mista Peter Obi suka shigar, kotun kolin ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta yanke a ranar 6 ga watan Satumba, inda ta tabbatar da ayyana Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya.

Hukuncin da kotun koli ta yanke, ba wai kawai ya kawo karshen duk wasu kararraki da suka shafi zaben shugaban kasa ba, har ma da tabbatar da aikin shugaban kasa na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

Ayyukan sun hada da samar da ingantacciyar shugabanci, samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya wanda hakan ta sa aka cire tallafin man fetur da kuma dawo da darajar naira, wanda gwamnatin Tinubu ta fara tun daga farkon lamari.

Sai dai babban kalubalen da ke fuskantar ‘yan Nijeriya sun hada da rashin zaman lafiya, rashin samun ci gaba, ayyukan ‘yan bindiga da kuma cin hanci da rashawa.

Kamar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke cewa, “idan ba mu yaki ci hanci da rashawa ba, to zai kashe mu “. Cin hanci da rashawa kamar wutar daji ce da ke cin zukatan ‘yan Nijeriya. Babu wani bangare na rayuwar ‘yan Nijeriya da cin hanci bai dabaibaye ba.

Domin haka, dole ne gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen karfafa yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin yakin neman zabe, Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin sake farfado da darajar Nijeriya.

Lallai idan har ‘yan Nijeriya za su ga sauyi, to dole ne Tinubu ya tashi tsaye wajen inganta gwamnatinsa da kuma yaki da cin hanci da rashawa a kowani bangare. Mafi yawancin mutane sun yi kara ga shugaban kasa ya yi kokarin gudanar da shugabanci nagari ta yadda zai iya farfado da darajar Nijeriya a idon duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Tsaro: Bai Wa Al’umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

Tsaro: Bai Wa Al'umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

LABARAI MASU NASABA

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.