• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Darikar Confucius ta ƙayyade cewa “ya kamata mu nemi jituwa a cikin bambance-bambance kuma kada mu yi wa wasu abin da ba za mu so a yi mana ba”. Burin kasar Sin shi ne ta samar da daidaito a wannan duniyar da ke cike da bambance-bambance. 

Duniyar tana daɗa dunkulewa waje guda tare da dogaro da juna, dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin ƙasashe ta zama abu mai muhimmanci ga bunƙasar tattalin arziki, haɗin gwiwar duniya, da kwanciyar hankali na jama’ar duniya.

  • Cinikayyar Albarkatun Gona Na Kasar Sin Da Kasashen Ketare Ta Karu Da Kaso 6.4 Bisa Dari A Rabin Shekarar Bana 

A kowace shekara, shugabannin gwamnatoci da galibin ministocin zartaswa na yin taro don tattaunawa kan batutuwan da suka shafi ƙasa da ƙasa, da ƙarfafa amincewa da fahimtar juna. Shi ya sa wannan dabarar Amurka ta “de-risking” wato “a raba gari da Sin” ka iya haifar da sakamakon da bai dace da dabarun haɗin gwiwar da ake bukata ba. Kuma abin lura shi ne, ƙasar Sin ba kamar Amurka ba, Sin na da ikon samun wadata kuma tana baiwa sauran ƙasashen duniya damar ci gaba a cikin wadatar da ta samu.

Mu ɗauki harkallar Tesla a kasar Sin a misali, wani lamari ne mai muhimmanci. Maimakon hana Tesla walwala a kasuwan Sin – kamar yadda Amurka ta yi wa kamfanin Huawei kuma take ƙoƙarin yi wa Tiktok na Sin a maimakon haka, ta ba da yanayin kasuwanci mai kyau da kuma babbar dama ta kasuwanci ga babbar fasahar Amurka, wato kasancewar kamfanin Tesla a Sin wanda ya sanya ƙarin matsin lamba ga masana’antun motoci masu amfani da makamashin lantarki (EV) na cikin gida, amma hakan bai zama matsala ga ƙasar Sin ba saboda ta yi imanin cewa hajjar Sinawa da ta Amurkawa duk za su haɓaka kuma su yi nasara ta hanyar tsaftacciyar gasa. Idan da Sin ta kasance kamar Amurka ne, da kamfanoni irin su Apple, Microsoft, Boeing da Nvidia ba za su yi tasiri ko su samu nasara a babbar kasuwar duniya ba.

A bangaren siyasa kuma, rikicin siyasa a cikin Amurka ya kai wani mataki na tarihi —- ’yan jam’iyyar Democrat da Republican suna rashin jituwa kan kusan dukkanin manyan batutuwa, kamar yadda kacaniyar batun bashi na kwanan nan ya sake bayyanawa. Kuma wannan rikici ba kawai yana shafar jama’ar Amurka ba, har ma da sauran sassan duniya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A cikin wannan zamani na canji da rashin daidaito, kwanciyar hankali da ci gaban ƙasar Sin na nufin wadata da samun kasuwa mai girma, da ƙarin jari, da damar zabin kayayyaki masu inganci, da ƙarin damar yin haɗin gwiwa. Daga shekarar 2013 zuwa ta 2021, matsakaicin gudummawar da Sin ta bayar wajen ci gaban duniya ya haura da kashi 30 cikin ɗari, fiye da haɗin gwiwar kungiyar G7, kuma ta zama ta ɗaya a dukkan ƙasashe. Kasancewar ƙasar Sin kan gaba wajen tabbatar da haɗin kai wata albarka ce ga al’ummarta, amma kuma abin dogaro ga jama’ar sauran ƙasashe.

Amurka ta ayyana ƙasar Sin a matsayin abokiyar adawa yayin da ita ƙasar Sin ba ta da sha’awar ƙalubalantar Amurka game da tafiyar da lamurran da suka shafi ci gaban duniya, musamman fasahar zamani, kasuwanci da tattalin arziki. Tasirin Amurka a sauran ƙasashen duniya ne ke kara raguwa saboda tsarin siyasarta da bukatunta. Babu wanda za a zarga da sanyaya dangantakar Amurka da ƙasashen duniyar da ke adawa da irin tsarinta na “wariya da rarrabuwa” face zabin da Amurka ta yiwa kanta.

Kamar dai yadda Jeffrey Sachs, farfesa kuma darektan cibiyar raya ci gaba mai dorewa ta jami’ar Columbia, ya ce a dandalin dimokuradiyya na Athens 2022, ƙasar Sin ta samu nasarori masu ban mamaki a cikin shekaru 40 da suka gabata, don haka ya kamata mu “yi farin ciki da nasarorin da ƙasar Sin ta samu, ba wai mu tsorata ba.” (Yahaya Babs)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana

Next Post

Gwamnati Ta Gaggauta Bincike Kan Yunkurin Kaiwa Atiku Harin Ta’addanci — Frank

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

5 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

5 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

7 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

10 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

12 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

13 hours ago
Next Post
Babban Jami’in Yakin Neman Zaben Atiku A Abuja, Danladi Zhin, Ya Rasu Yana Da Shekaru 54

Gwamnati Ta Gaggauta Bincike Kan Yunkurin Kaiwa Atiku Harin Ta'addanci — Frank

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.