ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?

by CGTN Hausa
2 years ago
Isra'ila

A ranar Juma’a ne kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICJ) wanda aka fi sani da kotun duniya ta ba Isra’ila umarni guda shida dangane da kisan kiyashi da take yi a Gaza, amma babu batun tsagaita bude wuta a cikin umarnin a bayyane.

 

An sanar da matakin na gaggawa ne a daidai lokacin da kotun ta yi zama kan shari’ar kisan kiyashin da kasar Afirka ta Kudu ta shigar a kan Isra’ila, wanda ta saurari shaidu a farkon wannan watan. Afirka ta Kudu ta bayyana abin da Isra’ila ke aikatawa a Gaza a matsayin kisan kare dangi amma Isra’ila ta musanta zargin, tana mai cewa yakinta a Gaza ya samo asali ne daga yunkurin “kare kai”, kuma ya zama dole ta kawar da Hamas. Ta kuma jaddada cewa ba za ta kawo karshen yakin ba har sai ta cimma wannan buri.

ADVERTISEMENT
  • Micheal Keating: Kasar Sin Ba Barazanar Tattalin Arziki Ba Ce
  • Masana’antun Kauyukan Sin Sun Samu Ci Gaba Yadda Ya Kamata A Shekarar 2023

Kusan watanni hudu ke nan duniya tana kallon yadda ake ruguza Gaza, lamarin da ya haifar da rikicin jin kai da ba a taba ganin irinsa ba. Ba a taba ganin irin wannan zaluncin da gangan ba a duniya, tare da nuna kyama ga kimar dan Adam da rayuwar dan Adam, yayin da wasu daga cikin manyan kasashen duniya suka ci gaba da siyasantar da batun.

 

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Kotun duniya ta yi umarni ga Isra’la kamar haka, dole ne Isra’ila ta dauki duk matakan da za a iya dauka don hana aikata abubuwa kamar yadda aka zayyana a cikin mataki na 2 na yarjejeniyar hana kisan kare dangi ta 1948. Wanda ya kunshi hana kashe mambobin wata kungiya, hana haifar da cutarwa ta jiki ko ta hankali ga mambobin wannan kungiyar, hana haifar da yanayin rayuwa wadanda za su kai ga kawo karshen wanzuwar wata al’umma, da kuma hana aiwatar da ayyukan da aka tsara don hana haifuwa a cikin wannan rukunin mutane. Dole ne Isra’ila ta tabbatar da cewa sojojinta ba su aiwatar da ko daya daga cikin wadannan matakan ba ga Falasdinawa ba.

 

Umarnin ya ci gaba da cewa, dole ne Isra’ila ta hana tare da hukunta wani tunani ko jama’a da suka shirya yin kisan kare dangi dangane da mambobin kungiyar Falasdinu a zirin Gaza”. Dole ne Isra’ila ta tabbatar da isar da muhimman ayyuka da kuma muhimman kayan agajin jin kai ga fararen hula a Gaza. Dole ne Isra’ila ta hana lalata shaidun laifukan yaki a Gaza tare da ba da damar gudanar da bincike na gaskiya. Dole ne Isra’ila ta gabatar da rahoto kan duk matakan da ta dauka don yin biyayya ga matakan da kotun ta dauka a cikin wata daya da yanke hukuncin.

To tambayar ita ce, shin Isra’ila za ta yi biyayya ga kotun duniya dangane da wannan hukunci? Tuni dai Isra’ila ta halaka Falasdinawa sama da 26,000 a hare-haren da take kaiwa kan zirin Gaza. Tare da katse hanyoyin sadarwa, da ta samar da abinci da agajin jin kai, da magunguna da ruwan sha. (Muhammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
Next Post
Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

LABARAI MASU NASABA

APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.