ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

by CGTN Hausa
3 years ago
Afirka

A kwanakin nan, kotun kasa da kasa na MDD ta yanke hukunci kan wasu bukatu dake kunshe a cikin karar da kasar Afirka ta Kudu ta shigar bisa zargin kasar Isra ‘ila da aikata kisan kare dangi a yankin Gaza, inda kotun ta umarci Isra’ila da ta kawo karshen duk wani mataki na kisan kiyashi, da daukar matakan sassauta yanayin jin kai a yankin Gaza. Daga baya, a nasa bangare, shugaban hukumar kungiyar kasashen Afirka AU, Moussa Faki Mahamat, ya bayyana farin cikinsa bisa hukuncin da kotun ta yanke, inda ya ce matakin ya kare kwarjinin dokokin kasa da kasa.

Game da yakin da ake yi a yankin Gaza, kasashen Afirka sun bukaci a kare fararen hula, da tsagaita bude wuta, ta yadda za a samu damar daidaita rikicin ta hanyar lumana bisa ka’idojin kasa da kasa. Wannan ra’ayi ya zama daya da na kasar Sin. Da ma yayin da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ke ziyara a wasu kasashe 4 dake nahiyar Afirka a kwanakin baya, ya tattauna batun Falasdinu tare da bangarorin Masar da Tunisia, da kuma sakatariyar kungiyar kasashen Larabawa. A cewar Mista Wang, kasar Sin tana Allah wadai da duk wani matakin da zai lahanta fararen hula, da keta ka’idojin kasa da kasa, kana kasar tana goyon bayan yukurin magance tsanantar rikici, da neman dawo da zaman lafiya. Kamar dai yadda suke da ra’ayi daya dangane da yakin da ake yi tsakanin kasashen Rasha da Ukraine, kasar Sin da kasashen Afirka suna ci gaba da tsayawa kan wani bangare da zai tabbatar da zaman lafiya da adalci.

  • Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?
  • Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

A sa’i daya, kasar Amurka da wasu kawayenta na yammacin duniya sun yi na’am da matakan da kasar Isra’ila ta dauka na wai “kare kanta”, inda suka dinga samar da makamai da kudi ga bangaren Isra’ila, duk da cewa matakan sojojin Isra’ila sun riga sun haddasa asarar rayukan Falasdinawa fiye da 26,000, ciki har da yara fiye da 10,000, kuma Isra’ila ta kai hari kan asibitocin yankin Gaza, da neman lalata tsarin samar da abinci na yankin don haddasa yunwa a can, kuma tuni babban taron MDD ya zartas da kudurin tsagaita bude wuta a yankin Gaza bisa takardun amincewa guda 153 da kasashe daban daban suka jefa.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, wani abun da ya faru a kwanan nan shi ne, sakamakon yadda kasar Isra’ila ta zargi wasu ma’aikatan hukumar da ba da agaji ga ‘yan gudun hijira Falasdinawa ta MDD UNRWA da hannu a harin da aka kai Isra’ila, kasashe 10 da suka hada da Amurka, da Birtaniya, da Jamus, da dai sauransu, sun dakatar da samar da kudi ga hukumar, duk da cewa akwai mutane fiye da miliyan 2 a yankin Gaza da suke dogaro kan hukumar wajen samun kayayyakin rayuwa da suke bukata.

Yadda kasashen yamma suka karkata ga wani bangare maimakon nuna adalci, har ya fusata masanansu, inda Renad Mansour, mai nazarin harkokin yankin gabas ta tsakiya na cibiyar nazari ta Chatham ta kasar Birtaniya, ya rubuta wani labari a kwanan nan, cewa “Bayan da kotun duniya ta amince da ikon da take da shi na bin bahasin kasar Isra’ila kan yadda take aiwatar da kisan kare dangi a yankin Gaza, hakan ya yi kama da gurfanar da ‘tsare-tsaren duniya da aka kafa bisa wasu ka’idoji na tushe’ a gaban kuliya. ” A cewar Mista Mansour, cikin shekaru fiye da 10 da suka gabata, kasashen yamma su kan gudanar da matakan soja a duniya don kare moriyarsu, musamman ma a fannin siyasa, amma duk da haka suna fakewa da maganar “kare dimokuradiyya, da hakkin dan Adam, gami da ka’idojin kasa da kasa” don halatta ayyukansu. Sai dai a halin yanzu, mai kafa tsari yana bata tsari. Sakamakon yadda sojojin Isra’ila suke wa yankin Gaza zobe, da jefa dimbin boma-bomai a kan Fadasdinawa, ba za a ci gaba da yarda da maganar kasashen yamma, ta samun wani tsarin kasa da kasa da aka kafa bisa ka’idoji ba.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Hakika galibin kasashe ba su son yin biyayya ga kasashen da suke kokarin yin babakere a duniya, da dogaro kan wadanda ke da karfi. Maimakon haka, suna son ganin wani tsarin kasa da kasa mai adalci, wanda ya shafi bangarori da dama, da neman samun wani muhalli mai zaman lafiya da kwanciyar hankali da zai amfani ci gaban tattalin arziki. Wani abun da za a iya hanga yanzu shi ne, bisa rincabewar tsare-tsaren kasa da kasa da suka mai da kasashen yamma a matsayin jagora, tunani da murya da kasashen Afirka da kasar Sin suka gabatar za su taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa, gami da samar da gudunmowa a kai a kai ga yunkurin kare zaman lafiya da adalci a duniya. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Dennis Francis: Kasar Sin Ce Mai Jagorantar Kiyaye Ka’idodjin Bangarori Daban Daban Da Inganta Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Dennis Francis: Kasar Sin Ce Mai Jagorantar Kiyaye Ka'idodjin Bangarori Daban Daban Da Inganta Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.