ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afirka Da Sin Suna Da Matsaya Daya Wato Kare Zaman Lafiya Da Adalci

by CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

A kwanakin nan, kotun kasa da kasa na MDD ta yanke hukunci kan wasu bukatu dake kunshe a cikin karar da kasar Afirka ta Kudu ta shigar bisa zargin kasar Isra ‘ila da aikata kisan kare dangi a yankin Gaza, inda kotun ta umarci Isra’ila da ta kawo karshen duk wani mataki na kisan kiyashi, da daukar matakan sassauta yanayin jin kai a yankin Gaza. Daga baya, a nasa bangare, shugaban hukumar kungiyar kasashen Afirka AU, Moussa Faki Mahamat, ya bayyana farin cikinsa bisa hukuncin da kotun ta yanke, inda ya ce matakin ya kare kwarjinin dokokin kasa da kasa.

Game da yakin da ake yi a yankin Gaza, kasashen Afirka sun bukaci a kare fararen hula, da tsagaita bude wuta, ta yadda za a samu damar daidaita rikicin ta hanyar lumana bisa ka’idojin kasa da kasa. Wannan ra’ayi ya zama daya da na kasar Sin. Da ma yayin da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ke ziyara a wasu kasashe 4 dake nahiyar Afirka a kwanakin baya, ya tattauna batun Falasdinu tare da bangarorin Masar da Tunisia, da kuma sakatariyar kungiyar kasashen Larabawa. A cewar Mista Wang, kasar Sin tana Allah wadai da duk wani matakin da zai lahanta fararen hula, da keta ka’idojin kasa da kasa, kana kasar tana goyon bayan yukurin magance tsanantar rikici, da neman dawo da zaman lafiya. Kamar dai yadda suke da ra’ayi daya dangane da yakin da ake yi tsakanin kasashen Rasha da Ukraine, kasar Sin da kasashen Afirka suna ci gaba da tsayawa kan wani bangare da zai tabbatar da zaman lafiya da adalci.

  • Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?
  • Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

A sa’i daya, kasar Amurka da wasu kawayenta na yammacin duniya sun yi na’am da matakan da kasar Isra’ila ta dauka na wai “kare kanta”, inda suka dinga samar da makamai da kudi ga bangaren Isra’ila, duk da cewa matakan sojojin Isra’ila sun riga sun haddasa asarar rayukan Falasdinawa fiye da 26,000, ciki har da yara fiye da 10,000, kuma Isra’ila ta kai hari kan asibitocin yankin Gaza, da neman lalata tsarin samar da abinci na yankin don haddasa yunwa a can, kuma tuni babban taron MDD ya zartas da kudurin tsagaita bude wuta a yankin Gaza bisa takardun amincewa guda 153 da kasashe daban daban suka jefa.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, wani abun da ya faru a kwanan nan shi ne, sakamakon yadda kasar Isra’ila ta zargi wasu ma’aikatan hukumar da ba da agaji ga ‘yan gudun hijira Falasdinawa ta MDD UNRWA da hannu a harin da aka kai Isra’ila, kasashe 10 da suka hada da Amurka, da Birtaniya, da Jamus, da dai sauransu, sun dakatar da samar da kudi ga hukumar, duk da cewa akwai mutane fiye da miliyan 2 a yankin Gaza da suke dogaro kan hukumar wajen samun kayayyakin rayuwa da suke bukata.

Yadda kasashen yamma suka karkata ga wani bangare maimakon nuna adalci, har ya fusata masanansu, inda Renad Mansour, mai nazarin harkokin yankin gabas ta tsakiya na cibiyar nazari ta Chatham ta kasar Birtaniya, ya rubuta wani labari a kwanan nan, cewa “Bayan da kotun duniya ta amince da ikon da take da shi na bin bahasin kasar Isra’ila kan yadda take aiwatar da kisan kare dangi a yankin Gaza, hakan ya yi kama da gurfanar da ‘tsare-tsaren duniya da aka kafa bisa wasu ka’idoji na tushe’ a gaban kuliya. ” A cewar Mista Mansour, cikin shekaru fiye da 10 da suka gabata, kasashen yamma su kan gudanar da matakan soja a duniya don kare moriyarsu, musamman ma a fannin siyasa, amma duk da haka suna fakewa da maganar “kare dimokuradiyya, da hakkin dan Adam, gami da ka’idojin kasa da kasa” don halatta ayyukansu. Sai dai a halin yanzu, mai kafa tsari yana bata tsari. Sakamakon yadda sojojin Isra’ila suke wa yankin Gaza zobe, da jefa dimbin boma-bomai a kan Fadasdinawa, ba za a ci gaba da yarda da maganar kasashen yamma, ta samun wani tsarin kasa da kasa da aka kafa bisa ka’idoji ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Hakika galibin kasashe ba su son yin biyayya ga kasashen da suke kokarin yin babakere a duniya, da dogaro kan wadanda ke da karfi. Maimakon haka, suna son ganin wani tsarin kasa da kasa mai adalci, wanda ya shafi bangarori da dama, da neman samun wani muhalli mai zaman lafiya da kwanciyar hankali da zai amfani ci gaban tattalin arziki. Wani abun da za a iya hanga yanzu shi ne, bisa rincabewar tsare-tsaren kasa da kasa da suka mai da kasashen yamma a matsayin jagora, tunani da murya da kasashen Afirka da kasar Sin suka gabatar za su taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa, gami da samar da gudunmowa a kai a kai ga yunkurin kare zaman lafiya da adalci a duniya. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Dennis Francis: Kasar Sin Ce Mai Jagorantar Kiyaye Ka’idodjin Bangarori Daban Daban Da Inganta Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Dennis Francis: Kasar Sin Ce Mai Jagorantar Kiyaye Ka'idodjin Bangarori Daban Daban Da Inganta Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.