• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, yadda wasu manyan abubuwan da suka faru a kasar Amurka sun jawo hankalin kasa da kasa. Na farko shi ne yadda wani jirgin kasa ya kauce daga layin dogon da yake bi a jihar Ohio ta kasar, na biyu shi ne yadda ake zargin gwamnatin Biden da tsara shirin lalata bututun iskar gas da ke tsakanin Rasha da Turai, na uku kuma shi ne yadda kasar Amurka ta harbo wani balan-balan na kasar Sin da makami mai linzami, sai dai yadda gwamnatin kasar Amurka ke mayar da martani ga batutuwan da ma yadda kafofin watsa labarai na kasar ke ba da rahotanni suna ba jama’a mamaki.

Jirgin kasan da ya kauce daga kan layin dogo yana dauke da sinadarai masu guba, lamarin da ya gurbata muhallin wurin sakamakon yadda sashen kula da al’amuran gaggawa na wurin ya daidaita hadarin, inda mazauna wurin suka fara ciwon kai da nuna sauran alamu na rashin lafiya, baya ga kuma dimbin kifayen da aka gano sun mutu a cikin kogunan wurin.

A sa’i daya kuma, sanannen dan jarida na kasar Seymour Hersh ya fitar da wani rahoton bincike, inda ya zargi gwamnatin Joe Biden da lalata bututun jigilar iskar gas na Nord Stream, don neman cimma moriyar kanta. Wadannan manyan abubuwa ne da suka shafi rayuwar al’ummar kasar Amurka da ma sunan kasar, amma abin mamaki shi ne, gwamnatin Amurka da kuma manyan kafofin yada labarai na kasar duk sun yi shiru, a yayin da kuma suke ta rura wutar batun wai “balan-balan na kasar Sin”.

Shin me ya faru ga gwamnatin Amurka da kafofin watsa labarai na kasar?

Me ya sa suke iya ganin balan balan da ta ratsa sararin samaniyar kasar bisa kuskure wanda ke da tsayin mita 18,000 daga doron duniyarmu, amma sun kasa ganin gurbatacciyar hayakin da ke saman jihar Ohio? Me ya sa suke ta rura wutar zancen barazana daga sauran kasashe, amma kuma suka kawar da ido daga hakikanin abin da ke barazana ga lafiyar al’ummar kasar?

Labarai Masu Nasaba

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Me ya sa a farkon fashewar bututun Nord Stream, suka daga murya suka ce dole a hukunta wadanda suka aikata laifin, amma kuma suka yi shiru bayan da Seymour Hersh ya fitar da rahotonsa?

A game da wannan, mai fashin baki kan harkokin siyasar kasar Amurka Alex Krainer ya yi nuni da cewa, lokacin da Amurka ke kokarin rura wutar batun “balan-balan na kasar Sin, a daidai lokacin ne da jirgin kasan ya kauce daga kan layin dogo da kuma Seymour Hersh ya fitar da rahotonsa, kuma dalilin da ya sa ta yi hakan shi ne don kawar da hankalin al’umma daga hakikanin matsalolin da suke fuskanta.

To, ashe wasa da hankalin al’umma ke nan Amurka ke yi. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi

Next Post

Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

Related

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

39 minutes ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

2 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

3 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

4 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

5 hours ago
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
Daga Birnin Sin

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

1 day ago
Next Post
Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.