ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuɗɗan Da Sule Lamido Ya Gindaya Wa Jam’iyyar PDP A Wa’adin Kwana 10

by Leadership Hausa
2 weeks ago
Lamido

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bai wa jam’iyyar PDP wa’adin kwana 10 don warware rikicin cikin gida tare da rushe taron zaɓen da aka yi kwanan nan a Ibadan da kuma kafa kwamitin riƙon ƙwarya na ƙasa.

Lamido ya yi kiran a ranar Alhamis yayin da yake magana ga goya bayansa ciki har da tsofaffin shugabannin ƙananan hukumomi da tsofaffin kwamishinoni, da sauran shugabannin siyasa da aka naɗa wanda suka kai masa ziyara ta zumunci a ofishinsa na Sharada a Kano.

  • Shugabannin APC Da PDP Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamna Adeleke Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Ya bayyana damuwa game da rikicin da ke ci gaba da ruruwa a cikin jam’iyyar, yana mai cewa masu ruwa da tsaki na da dogon lokaci na warware matsalar PDP.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa matakan shari’ar da ya ɗauka ba don an haka masa tikitin takarar shugaban jam’iyyar ba ne, amma don ya kare muradun PDP da haƙƙinsa da aka take.

Ya dage cewa, a halin da ake ciki, Umar Damagum da Samuel Anyanwu suna nan a matsayin sahihan shugabannin jam’iyyar har zuwa lokacin da wa’adinsu zai kare a ranar 8 ga Disamba, 2025.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ya yi gargaɗin cewa barin jam’iyya ta ci gaba ba da tafiya a haka ba zai taɓa haifar da ɗa mai ido ba ga makomar masu neman muƙamai, masu riƙe da ofisoshi, da waɗanda ke shirin sake tsayawa takara.

Tsohon gwamnan ya yi kira ga shugabannin PDP su shirya taro na haɗin gwiwa don su fuskanci ƙalubalen jam’iyyar da gaskiya tare da mayar da ita zuwa matsayinta na gaskiya a siyasar ƙasar nan.

Har ila yau, ya buƙaci goya bayansa da su kasance cikin natsuwa da haƙuri har zuwa 8 ga Disamba don ganin yadda abubuwa za su kasance.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Ci Gaban Fasahar AI A Kasar Sin Ya Nuna Gazawar Matakan Amurka Na Tare Hanyar Sin

Ci Gaban Fasahar AI A Kasar Sin Ya Nuna Gazawar Matakan Amurka Na Tare Hanyar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.