• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

by Muhammad Ubale Kiru
2 months ago
Matarsa

Wato manufar wannan rubutu ita ce, ina so na zama uba da uwa ga matasanmu marasa iyaye, da kuma wanda ba su samu damar koyar rayuwa daga wajen iyayensu ba.

Abin bakin ciki al’ummar mu ta fi mai da hankali wajen yi wa mata fada da gyara, akan manta da maza. Shi ya sa lokaci zuwa lokaci nake rubuce-rubuce don na fadakar ko na wayar da kan matasa maza. Yau za mu tattauna akan wani batu: Wato idan matarka ta samu Juna biyu.

  • Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
  • Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Wani dan-uwa ya ce, Ya Muhammad, matata ta samu juna-biyu, kuma tun da ta samu, bama samun damar shiga “dakiñ canba”. Ya nuna damuwa sosai, kuma a matsayina na gogyaggye zan yi bayani akai zan kira ka don mu tattaunawa. Kuma Alhamdu lillah, na kira shi, kuma ya ji dadi sosai, kuma ya fahimci sakon. Na ce duk da haka ya kamata a wayar da kai don kar a bar ‘yan baya.

Ya kai matashi, yana da kyau ka sani. Ita mace a duk sanda ta samu juna-biyu, wannan lokaci, shi ne lokaci mafi wuya da kalubale a wurinta. Allah ne ya tsara haka, ka ga mace ta shiga wani mawuyacin hali musamman a wata ukun farko, wato tana cikin watanni uku na farko.

A wannan lokaci za ka lura cewa ba ta son abubuwa da yawa, kai wata ko kamshin turarenka ba ta so. Wata ko kusa da ita ba ta so ka zo. Sannan za ta yi ta rashin lafiya da son kwanciya. Wata sai ta yi kamar za ta mutu, ka ga ta kyar take iya tashi. Sannan shi kansa kauracewa kwanciya a wannan lokacin zai iya zama alkhairi.

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

Domin kuwa wasu matan kwanciya kan iya zama sanadi na lalacewar cikin. So, akan ce ma a rage ko a bari a watanni uku na farkon ciki. Don haka idan ka ga wadannan matsalolin kar ka ce wai kirkira take, ko da gangan take. Ba gaskiya bane. Lalura ce babba, kuma da take bukatar kallo na musamman.

Idan kaga wannan lokacin yazo, anan ne ake so ka nuna soyayyarka, da kulawarka, da taimakonka. Wajibi ka bata hadin-kai don ta wuce wannan watanni uku na farko din. Domin cikin jikinta a wannan lokacin kamar akan siratsi yake, duk abinda aka ce ana halittarta ’yan Adam a cikinsa ai yaga taka kansa. Komai zai iya faruwa. Namiji dan kirki shine sai kaga ya shiga kokarin yin hidimar gida da kansa. Shine wanke wanke, shara, girki, kaye kaye da sauransu. Sannan duk abinda tace tana sha’awa indai da hali a saya mata. Wallahi ba daga ita bane, daga yanayin cikin ne. Za Mu Ci Gaba Mako Mai Idan Allah Ya Kai Mu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

October 3, 2025
Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

September 26, 2025
Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata
Madubin Rayuwa

Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

September 21, 2025
Next Post
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.