ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

by Muhammad Ubale Kiru
9 months ago
Matarsa

Wato manufar wannan rubutu ita ce, ina so na zama uba da uwa ga matasanmu marasa iyaye, da kuma wanda ba su samu damar koyar rayuwa daga wajen iyayensu ba.

Abin bakin ciki al’ummar mu ta fi mai da hankali wajen yi wa mata fada da gyara, akan manta da maza. Shi ya sa lokaci zuwa lokaci nake rubuce-rubuce don na fadakar ko na wayar da kan matasa maza. Yau za mu tattauna akan wani batu: Wato idan matarka ta samu Juna biyu.

  • Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
  • Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Wani dan-uwa ya ce, Ya Muhammad, matata ta samu juna-biyu, kuma tun da ta samu, bama samun damar shiga “dakiñ canba”. Ya nuna damuwa sosai, kuma a matsayina na gogyaggye zan yi bayani akai zan kira ka don mu tattaunawa. Kuma Alhamdu lillah, na kira shi, kuma ya ji dadi sosai, kuma ya fahimci sakon. Na ce duk da haka ya kamata a wayar da kai don kar a bar ‘yan baya.

ADVERTISEMENT

Ya kai matashi, yana da kyau ka sani. Ita mace a duk sanda ta samu juna-biyu, wannan lokaci, shi ne lokaci mafi wuya da kalubale a wurinta. Allah ne ya tsara haka, ka ga mace ta shiga wani mawuyacin hali musamman a wata ukun farko, wato tana cikin watanni uku na farko.

A wannan lokaci za ka lura cewa ba ta son abubuwa da yawa, kai wata ko kamshin turarenka ba ta so. Wata ko kusa da ita ba ta so ka zo. Sannan za ta yi ta rashin lafiya da son kwanciya. Wata sai ta yi kamar za ta mutu, ka ga ta kyar take iya tashi. Sannan shi kansa kauracewa kwanciya a wannan lokacin zai iya zama alkhairi.

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

Domin kuwa wasu matan kwanciya kan iya zama sanadi na lalacewar cikin. So, akan ce ma a rage ko a bari a watanni uku na farkon ciki. Don haka idan ka ga wadannan matsalolin kar ka ce wai kirkira take, ko da gangan take. Ba gaskiya bane. Lalura ce babba, kuma da take bukatar kallo na musamman.

Idan kaga wannan lokacin yazo, anan ne ake so ka nuna soyayyarka, da kulawarka, da taimakonka. Wajibi ka bata hadin-kai don ta wuce wannan watanni uku na farko din. Domin cikin jikinta a wannan lokacin kamar akan siratsi yake, duk abinda aka ce ana halittarta ’yan Adam a cikinsa ai yaga taka kansa. Komai zai iya faruwa. Namiji dan kirki shine sai kaga ya shiga kokarin yin hidimar gida da kansa. Shine wanke wanke, shara, girki, kaye kaye da sauransu. Sannan duk abinda tace tana sha’awa indai da hali a saya mata. Wallahi ba daga ita bane, daga yanayin cikin ne. Za Mu Ci Gaba Mako Mai Idan Allah Ya Kai Mu

Matarsa
Muhammad Ubale Kiru
+ postsBio

    MASU ALAKA

    GORON JUMA’A
    Madubin Rayuwa

    GORON JUMA’A

    May 1, 2026
    GORON JUMA’A
    Madubin Rayuwa

    GORON JUMA’A

    March 20, 2026
    GORON JUMA’A
    Madubin Rayuwa

    GORON JUMA’A

    March 13, 2026
    Next Post
    Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

    Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno - Atiku

    LABARAI MASU NASABA

    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

    June 4, 2026
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

    June 4, 2026
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

    June 4, 2026
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

    June 3, 2026
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

    June 3, 2026
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

    June 3, 2026
    Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

    June 3, 2026
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

    June 3, 2026
    Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

    Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

    June 3, 2026
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

    June 3, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.