• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kun taba kai ziyara a tashar jiragen ruwa ta Lekki dake Legas, Najeriya? Wata sabuwar tashar zamani ce, da Najeriya da Sin, da sauran bangarorin kasa da kasa, suka gina a hadin gwiwarsu, wadda ta kasance tashar jiragen ruwa mafi girma ta Najeriya. Ban da haka, bisa matsayinta na tasha mai kunshe da mafi yawan fasahohin zamani a yammacin Afirka, tashar jiragen ruwa ta Lekki na taka rawar gani a fagen zamanantarwa da ci gaban tattalin arzikin Najeriya, da na sauran kasashe makwabtanta. Sai dai idan an tantance dalilan da suka haifar da tashar, za a ga akwai tallafin da aka samu daga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI) da kasar Sin ta kaddamar.

 

Akwai dimbin abokai da suka yi mana tambaya kan ma’anar taken shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”. Hakika wannan suna yana da alaka da muhimman tsoffin hanyoyin ciniki da suka hada kasar Sin da sauran kasashe a tarihi, wato Hanyar Siliki, da Hanyar Siliki dake Kan Teku. Dalilin da ya sa aka ba wata sabuwar shawara sunan wasu tsoffin hanyoyi, shi ne domin muhimmiyar rawar da tsoffin hanyoyin suka taka ta fuskar raya tattalin arzikin duniya, inda a maimakon dogaro kan karfin makamai, da kaddamar da yaki, aka yi amfani da ayarin rakuma, da jiragen ruwan dakon kaya, wajen karfafa cudanyar ciniki, da al’adu, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

  • CMG Ya Gabatar Da Alamar Bayyana Kyakyyawar Fata Ta Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiya Ta Kasar Sin

Shawarar BRI ta gaji ruhin tsoffin hanyoyin ciniki da aka kafa a tarihi, inda ta samar da damammaki na samun ci gaba ga duniya, abin da ya sa ta samun karbuwa sosai. Idan muka dauki nahiyar Afirka a matsayin misali, tun bayan da kasar Sin ta kaddamar da shawarar BRI a shekarar 2013, har zuwa yanzu, kasashe 52 dake nahiyar Afirka da kwamitin kungiyar kasashen Afirka ta AU, dukkansu sun kulla yarjeniyoyi na hadin gwiwa tare da kasar Sin, a karkashin shawarar. Ta haka, an samu dimbin sakamako masu gamsarwa, inda a fannin ciniki aka samu ci gaba sosai, ko a shekarar bara kadai ma, yawan cinikin da kasar Sin ta yi tare da kusan rabin kasashen dake nahiyar Afirka ya karu da fiye da kaso 10%. Bayan haka, kasar Sin ta zama kasar da ta zuba mafi yawan jari ga kasashen Afirka, kana a cikin shekaru 3 da suka wuce, kamfanoninta suka samar da guraben aikin yi fiye da miliyan 1 da dubu dari ga kasashen Afirka. Haka zalika, an gina dimbin kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, bisa hadin gwiwa da kasar Sin.

 

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da cewa, BRI za ta ci gaba da haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki? A jiya Litinin, an gudanar da taron karawa juna sani kan aikin aiwatar da BRI karo na 4 a birnin Beijing na kasar Sin, inda shugaban kasar Xi Jinping ya bayyana tsarin da za a bi wajen ci gaba da aiwatar da shawarar BRI a nan gaba. Cikin jawabinsa, ya yi bayanai masu muhimmanci, kamar su “kokarin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya” da “tsayawa kan manufar tattaunawa tare da kasashe daban daban, da yin aiki bisa hadin kai tare da su, gami da raba damar cin moriya tare da su”, da dai makamantansu. Abin lura shi ne, wannan taro na manyan jami’an kasar Sin ne, maimakon na kasa da kasa, don haka, maganar da shugaba Xi ya fada, ba da umarni ne ga jami’an Sin, maimaikon tallar wata manufar Sin ga kasashe daban daban. Amma duk da haka, shugaban na kasar Sin bai taba nuna son kai ba ko kadan. Kafin ya ambaci batun kare moriyar kasar Sin, ya jaddada bukatar samar da karin alfanu ga kasashen da suke cikin shawarar BRI.

 

A ganina, zamanin da muke ciki ya baiwa BRI karin muhimmanci. Saboda a halin yanzu, an fi nuna ra’ayi na son kai a duniyarmu, inda dimbin kasashe ke son daukar matakan radin kai, da bata huldar ciniki, da kin dunkulewar tattalin arzikin duniya. Sai dai duk da haka, BRI na ci gaba da samar da wani yanayi mai yakini a duniya, inda take kokarin tabbatar da samun zaman lafiya, da hadin kai, da kare moriyar bangarori daban daban, da neman samun ci gaba tare. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Kone Shaguna A Kasuwar Yobe

Next Post

Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

Related

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

15 minutes ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

26 minutes ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

2 hours ago
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

4 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

21 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

22 hours ago
Next Post
Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.