• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kun taba kai ziyara a tashar jiragen ruwa ta Lekki dake Legas, Najeriya? Wata sabuwar tashar zamani ce, da Najeriya da Sin, da sauran bangarorin kasa da kasa, suka gina a hadin gwiwarsu, wadda ta kasance tashar jiragen ruwa mafi girma ta Najeriya. Ban da haka, bisa matsayinta na tasha mai kunshe da mafi yawan fasahohin zamani a yammacin Afirka, tashar jiragen ruwa ta Lekki na taka rawar gani a fagen zamanantarwa da ci gaban tattalin arzikin Najeriya, da na sauran kasashe makwabtanta. Sai dai idan an tantance dalilan da suka haifar da tashar, za a ga akwai tallafin da aka samu daga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI) da kasar Sin ta kaddamar.

 

Akwai dimbin abokai da suka yi mana tambaya kan ma’anar taken shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”. Hakika wannan suna yana da alaka da muhimman tsoffin hanyoyin ciniki da suka hada kasar Sin da sauran kasashe a tarihi, wato Hanyar Siliki, da Hanyar Siliki dake Kan Teku. Dalilin da ya sa aka ba wata sabuwar shawara sunan wasu tsoffin hanyoyi, shi ne domin muhimmiyar rawar da tsoffin hanyoyin suka taka ta fuskar raya tattalin arzikin duniya, inda a maimakon dogaro kan karfin makamai, da kaddamar da yaki, aka yi amfani da ayarin rakuma, da jiragen ruwan dakon kaya, wajen karfafa cudanyar ciniki, da al’adu, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

  • CMG Ya Gabatar Da Alamar Bayyana Kyakyyawar Fata Ta Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiya Ta Kasar Sin

Shawarar BRI ta gaji ruhin tsoffin hanyoyin ciniki da aka kafa a tarihi, inda ta samar da damammaki na samun ci gaba ga duniya, abin da ya sa ta samun karbuwa sosai. Idan muka dauki nahiyar Afirka a matsayin misali, tun bayan da kasar Sin ta kaddamar da shawarar BRI a shekarar 2013, har zuwa yanzu, kasashe 52 dake nahiyar Afirka da kwamitin kungiyar kasashen Afirka ta AU, dukkansu sun kulla yarjeniyoyi na hadin gwiwa tare da kasar Sin, a karkashin shawarar. Ta haka, an samu dimbin sakamako masu gamsarwa, inda a fannin ciniki aka samu ci gaba sosai, ko a shekarar bara kadai ma, yawan cinikin da kasar Sin ta yi tare da kusan rabin kasashen dake nahiyar Afirka ya karu da fiye da kaso 10%. Bayan haka, kasar Sin ta zama kasar da ta zuba mafi yawan jari ga kasashen Afirka, kana a cikin shekaru 3 da suka wuce, kamfanoninta suka samar da guraben aikin yi fiye da miliyan 1 da dubu dari ga kasashen Afirka. Haka zalika, an gina dimbin kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, bisa hadin gwiwa da kasar Sin.

 

Labarai Masu Nasaba

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da cewa, BRI za ta ci gaba da haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki? A jiya Litinin, an gudanar da taron karawa juna sani kan aikin aiwatar da BRI karo na 4 a birnin Beijing na kasar Sin, inda shugaban kasar Xi Jinping ya bayyana tsarin da za a bi wajen ci gaba da aiwatar da shawarar BRI a nan gaba. Cikin jawabinsa, ya yi bayanai masu muhimmanci, kamar su “kokarin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya” da “tsayawa kan manufar tattaunawa tare da kasashe daban daban, da yin aiki bisa hadin kai tare da su, gami da raba damar cin moriya tare da su”, da dai makamantansu. Abin lura shi ne, wannan taro na manyan jami’an kasar Sin ne, maimakon na kasa da kasa, don haka, maganar da shugaba Xi ya fada, ba da umarni ne ga jami’an Sin, maimaikon tallar wata manufar Sin ga kasashe daban daban. Amma duk da haka, shugaban na kasar Sin bai taba nuna son kai ba ko kadan. Kafin ya ambaci batun kare moriyar kasar Sin, ya jaddada bukatar samar da karin alfanu ga kasashen da suke cikin shawarar BRI.

 

A ganina, zamanin da muke ciki ya baiwa BRI karin muhimmanci. Saboda a halin yanzu, an fi nuna ra’ayi na son kai a duniyarmu, inda dimbin kasashe ke son daukar matakan radin kai, da bata huldar ciniki, da kin dunkulewar tattalin arzikin duniya. Sai dai duk da haka, BRI na ci gaba da samar da wani yanayi mai yakini a duniya, inda take kokarin tabbatar da samun zaman lafiya, da hadin kai, da kare moriyar bangarori daban daban, da neman samun ci gaba tare. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Kone Shaguna A Kasuwar Yobe

Next Post

Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

Related

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma
Daga Birnin Sin

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

15 hours ago
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

17 hours ago
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 
Daga Birnin Sin

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

19 hours ago
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci
Daga Birnin Sin

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

21 hours ago
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

1 day ago
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

1 day ago
Next Post
Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

LABARAI MASU NASABA

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

September 4, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

September 4, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

September 4, 2025
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

September 4, 2025
An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

September 4, 2025
Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.