• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Kasar Sin Game Da Tsaron Kasa Da Kasa Ta Ingiza Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya, In Ji Masana

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarar Kasar Sin Game Da Tsaron Kasa Da Kasa Ta Ingiza Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya, In Ji Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai fashin baki game da alakar kasa da kasa dan asalin kasar Zimbabwe Gibson Nyikadzino, ya ce shawarar da kasar Sin ta gabatar game da tsaron kasa da kasa ko GSI a takaice, ta ingiza burin da ake da shi na wanzar da zaman lafiya da tsaro, da daidaito, tare da sanya kyakkyawan karsashi ga duniya baki daya.

Nyikadzino, wanda ya zanta da kafar dillancin labarai ta Xinhua, ya ce Sin ta zamo babban jigo a fannin wanzar da zaman lafiya da tsaro, a gabar da duniya ke fuskantar manyan kalubaloli.

  • Lula: Duniya Na Bukatar Kasar Sin

A watan Afrilun shekarar 2022 da ta gabata ne kasar Sin ta gabatar da shawarar GSI, wadda ke da nufin samar da sabuwar hanyar wanzar da tsaro, ta hanyar tattaunawa maimakon yin fito-na-fito, da hadin gwiwa maimakon kafa wani gungu, da cimma moriyar juna maimakon salon “wani ya samu wani ya rasa”.

Masanin ya kara da cewa, yayin da manufofin tsaro na kasashen yamma ke mayar da hankali ga amfani da matakan soji wajen shawo kan rigingimu, a daya bangaren Sin ta gabatar da shawarar wanzar da zaman lafiya mai nagarta, wadda za ta ba da gudummawa ga wanzuwar tsaron duniya.

Masanin ya ce ya damu matuka da tasirin manufofin harkokin wajen kasashen yamma, masu ba da karfi ga matakan soji, bisa irin mummunan tasirin da suka yi a kasashe irin su Afghanistan, da Iraki, da Syria da Libya. A cewar sa, irin wadannan manufofi an kirkire su ne da nufin amfanar da kamfanonin kirar makamai, matakin da ya yi matukar illata zaman lafiyan duniya.

Labarai Masu Nasaba

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Kalaman na Nyikadzino dai sun yi daidai da na masanin tattalin arziki dan kasar ta Zimbabwe Paul Musodza, wanda yayin zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya bayyana shawarar GSI din a matsayin wadda ta bunkasa zaman lafiya, da ci gaba mai dorewa a duniya baki daya.

Musodza ya kara da cewa, baya ga shawarar GSI, kasar Sin ta kuma gabatar da shawarar ziri daya da hanya daya, da shawarar bunkasa ci gaban duniya, da kuma shawarar wayewar kan duniya baki daya.

Daga nan sai ya jinjinawa tasirin shawarwarin na Sin, ganin irin gajiya da kasashen nahiyar Afirka, da ma na sauran sassan duniya za su ci daga gare su. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bai Kamata Japan Ta Zuba Ruwan Da Sinadarin Nukiliya Ya Gurbata Cikin Tekun Pasifik Ba

Next Post

Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?

Related

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

1 hour ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

2 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

2 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

5 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

5 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

7 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?

Me Ya Sa Shugabannin Kasa Da Kasa Da Manyan ‘Yan Kasuwa Suka Yi Ta Kawo Ziyara Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.