• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta – Hauwa Yusuf

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
in Nishadi
0
Shawarata Ga Duk Wacce Za Ta Shiga Fim Ta Nemi Izinin Iyayenta – Hauwa Yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitacciyar Jarumar da ke haskawa a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood musamman cikin shiri mai dogon zango na Lu’u Lu’u, da IZZAR SO, Jarumar da aka fi sani da suna KHADIJA a cikin shirin Lu’u Lu’u wato HAUWA YUSUF MUHD, Ta bayyanawa masu karatu yadda farkon fara fim din ta ya kasance, tare da dalilinta na shiga harkar fim, gami da cewa, duk wacce za ta shiga harkar fim ta kasance da sanin iyayenta. Jarumar ta kuma yi kira ga Gwamnati dangane da ci gaban masana’antar Kannywood, har ma da wasu batutuwan da suka shafi rayuwarta ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:

Masu karatu za su so sanin cikakken sunanki tare da dan takaitaccen tarihinki.

Sunana Hauwa’u Yusuf Moh’d wacce aka fi sani da Khadija a cikin shirin LU’U LU’U. An haife ni a cikin garin Katsina a unguwar ‘Rafin Dadi’ dake cikin garin Katsina, a 1999 na kammala karatuna a 2017, Alhamdulillah ina da Izu 45 a makaratar Islamiya.

Ma sha Allah. To me ya ja hankalinki har kika tsunduma cikin harkar fim?

Abin da ya ja hankalina na shiga harkar fim saboda ina so in fadakar, kuma in tunatar wal’ummar Musulmi na duniya baki daya, hakan kuma ta samu nasaba da tun ina yarinya nake son masana’antar shirya fina-finai wacce aka fi sani da Kannywood.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Shawarata
Jaruma Hauwa Yusuf

Za ki yi kamar shekara nawa cikin masana’antar Kannywood?

Zan iya kai kamar kimanin shekara hudu 4 a masana’antar.

Nawa ne adadin fina-finan da kika yi?

Na yi fim mai suna Mubarek da Salmanu da Sai Mai Mota, Dan Chacha, Kansilan Kauye, da dai sauransu ba zan iya tuna adadinsu ba don na manta wasu, sai kuma wanda muke cikinsa a yanzu LU’U LU’U da IZZAR SO da HADARIN SO da SILAR SO duka ‘mai dogon zango’ ne.

A wanne fim kika fara fitowa, da wanne kika fara?

Na fara da Mubarek da Salmanu duk lokaci daya ne na fara da su.

Shawarata
Jaruma Hauwa Yusuf

Ya farkon farawarki ya kasance kasancewar shi ne farko a lokacin?

Gaskiya ko da na fara mutane da dama sun yi mamaki musamman da aka ce musu farkon farawa ne, sakamakon akwai abin a raina, kuma ina so shi ya sa ban ji wani dar a jikina ba.

Ko akwai abin da ya baki wuya a lokacin da za ki fara?

Gaskiya ban ji wuyar komai ba, sai dai jiki d a jini wanda baka saba da shi ba. Gaskiya ban sa komai a raina ba, komai aka ce na yi zan iya yi shi in sha Allah.

Toh ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?

Cikin sauki ba tare da wata wahala ba, sakamakon ina da yaya ko in ce yayye a cikin masana’antar.

To batun iyaye kuma fa, Lokacin da kika sanar musu cewa kina sha’awar shiga harkar fim, ko akwai wani kalubale da kika samu daga gare su?

 Gaskiya ban samu ba, sai ma goyen baya da suka bani, sai dai a ce ko cikin ‘yan uwa a samu abin da ba a rasa ba.

A gaba daya fina-finan da kika yi idan aka ce ki fadi bakandamiyarki wanne za ki ce?

Zan iya cewa LU’U LU’U, saboda yanzu da shi ne aka fi sanina kuma aka fi kallon sa bisa ga na baya da suka wuce.

Shawarata
Jaruma Hauwa Yusuf

Wace rawa kika taka a cikin shirin Ku’u Lu’u?

Ni ce nake jan fim din ko kuma in ce miki ni ce ‘star’ a fim din labarin a kaina yake zan iya ce miki a takaice.

Lokacin da za a fara shirin Lu’u lu’u ke ce kika zabi fitowa a matsayin tauraruwar shirin ko kuwa wadanda suka shirya shirin ne suka ga kin dace da matsayin fitowa Tauraruwa?

A a! ba ni na zaba ba, sun tara masu ba da umarni da yawa da kuma masu daukar nauyin shiri suka ga na cancanci a sani matsayin tauraruwar shirin, da kuma zabin Allah.

Wanne irin farin ciki kika yi lokacin da kika ji cewa ke ce za ki zamo babbar tauraruwa a shirin?

Gaskiya na ji dadi sosai duk da ba shi kadai bane fim din da na ja sai dai a ce shi wannan me dogon zango ne ya sha bamban da na kasuwa da kuma gidajen TB kuma ina alfarahari da shirin fim din LU’U LU’U a ko da wane lokaci.

Na ji kin ce kin fito a shirin Izzar so, shi wacce rawa kika taka cikin shirin?

A cikin shirin fim din izzar so na taka rawa matsayin kanwar wanda ya tsinci Umar Hashim ne wato Alawiyya.

Ko akwai wani kalubale da kika taba fuskanta game da wannan sana’ar taki ta fim?

Ai faruwar kalubale nasara ce, kuma ba a fadarsa sai dai a bashi baya duk abin da ya wuce ya riga da ya wuce sai dai mu tunkari gaba.

To ya batun nasarori fa wanne irin nasarori kika samu game da fim?

Nasarori ma sai dai mu ce Alhamdulilahi Allah Ya kara wa Annabi daraja (S.A.W)

Me kike son cimma game da fim?

Ina so na kai matakin da kowa ya kai idan Allah ya amince, saboda komai da yardar mahalicci yake zuwa.

Ya kika dauki fim a wajenki?

Sana’a da kuma kaunar masana’antar idan na ce sha’awa na lokaci kalilan ne.

Wace ce babbar kawarki a Kannywood?

Kowa kawata ce.

Da wa kika fi so a hadaki a fim?

Da kowa ina jin dadin aiki, amma ina so a hada ni da Salisu S. Fulani.

Kar fa ki sa mutane su ce ko dai soyayyar ta gaske ce?

A a ko daya ba soyayya, sai dai ta Yaya da kanwarsa, amma ba ta gaske ba ce.

Ko kina da iyayen gida a kannywood?

Eh, Ina da su, akwai; Isah Bawa Doro, Balarabe Kabeer, Lawal Agga Sama’il Abba.

To, ya batun soyayya fa, ko akwai wani da ya taba kwanta miki a rai cikin masana’antar da har ta kai da kin fara soyayya da shi?

Babu ko daya ina da wanda nake so ni ma a gefe. Yaushe za ki aure?

Lokacin da Allah ya amince.

Shawarata
Jaruma Hauwa Yusuf

Wanne irin namiji kike son aura?

Ina son namiji mai tsoron Allah, mai addini, masanin Alkur’ani da Hadissan Manzon Allah mai kiyaye hakkin addinin Muslunci.

Bayan fim kina wata sana’ar ne?

Eh ina sana’ar kwalliya.

Akwai wani waje da kika bude wanda ki ke kwalliyar, ko kuwa a gida kike yi?

A gida nake yi, ina da burin budewa in Sha Allahu a nan gaba.

Ya kike iya hada sana’arki ta fim da ta kwalliya?

Lafiya kalau kuwa ai ba kullum ake fita aikin fim ba, haka ita ma kwalliyar, kuma ba su taba hade mun ba.

Wanne abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ki taba iya mantawa da shi a rayuwarki ba?

Ba zan taba manwata da ranar da mahaifina ya rasu ba, a kullum ina jin rashinshi sabo a zuciyata farin cikin da ba zan manta da shi ba shi ne; kullum da nake kallon mahaifiyata cikin lafiya da amincin Annabi.

Me ya fi sa ki farin ciki a rayuwa?

In ganni zaune cikin ‘yan uwana ga kuma jikokin gidanmu, ina jin farin ciki sosai shi ma.

Me za ki ce ga masu kokarin shiga harkar fim, har ma da wadanda suke ciki?

Ina so duk wacce za ta shiga harkar fim ta kasance da sanin iyayenta ta shigo domin alfarmar iyaye aka fi so fiye da daudar duniya. Mu kuma da muke cikinta Allah ya kara hada kanmu, Allah ya kara bamu zaman lafiya f i y e da yadda muke yanzu.

Me za ki ce da masoyanki?

Ina yi musu fatan alkairi, ina kuma kaunarsu fiye da yadda suke sona Allah ya bar kauna a tsakaninmu, Allah ya zaunar da kasarmu lafiya don Alfarmar Annabi.

Shawarata
Jaruma Hauwa Yusuf

Ko akwai wani kira da za ki yi ga gwamnati game da harkar fim?

Kira na ga gwamnati shi ne; kara wa kwarin giwa da mu da furodusashinmu da kuma daraktocinmu, duk wani kiran da muke yi ga gwamnati ne, sannan ina yin mata fatan alkhairi.

Me za ki ce da makarantar wannan shafi na Rumbun Nishadi da ita kanta Jaridar LEADERSHIP Hausa?

Ina yi musu fatan alkhairi Allah ya kara daga darajar wannan gidan Jarida ta LEADERSHIP Hausa, da kuma shafin Rumbun Nishadi, Allah ya kara muku kwarin gwiwa ga jajircewarku, kuma Allah ya cika muku burinku na alkhairi amen.

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Eh akwai su, ina mika gaisuwata musamman ga Ogana Isah Bawa Doro da kuma Yayana Ibrahim Bala, sannan Lawal Ibrahim Gungu, Balarabe Kabir, Sama’ila Abbah ina yi musu kyakkyawar gaisuwa ta musamman. Muna godiya Malama Hauwa Ni ma na gode.

Shawarata
Jaruma Hauwa Yusuf

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FimJarumaJarumaiNishadiTauraruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Karbe Filin Jirgin Saman Gombe

Next Post

Sakacin Maigida Nasa Batagari Matsala A Gaba (2)

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

2 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 week ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Sakacin Maigida Nasa Batagari Matsala A Gaba (2)

Sakacin Maigida Nasa Batagari Matsala A Gaba (2)

LABARAI MASU NASABA

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.