• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kasar Sin Sun Dace Da Bukatun Tabbatar Da Tsaron Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarwarin Kasar Sin Sun Dace Da Bukatun Tabbatar Da Tsaron Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin kammala taro kan tsaro na Shangri-La a Singapore a ranar Lahadi, tawagar kasar Sin ta ce kasar ta tabbatar da kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa bisa ayyukanta masu amfani, ta yadda ta ba da gudummawa wajen samar da tsaron jama’a da kyautata zamantakewar kasa da kasa.

Tabbas salon kasar Sin game da batun tsaro da ma sauran batutuwa, ya fita daban da na sauran kasashen da suka ci gaba, domin ba ta kasance mai tayar da fitina ko takala ko kara rura wutar rikici ba, maimakon haka, ta kasance mai sulhu tsakanin bangarorin da ba sa jituwa, kuma mai kira da a hau teburin tattaunawa da tabbatar da adalci da kuma warware matsaloli tun daga tushe.

  • Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara
  • Ƴan Bindigar Nijeriya Sun Kai Hari Ƙasar Niger

A ko da yaushe ta kan yi la’akari da moriyar da halaltattun hakkokin al’ummomin kasa da kasa, haka kuma ba ta sanya siyasa cikin al’ummarn da suka shafi rayuwar fararen hula. Yanayin zaman lafiya da al’ummar kasar ke morewa, ya isa tabbatar da cewa, hanyar kasar Sin na neman tsaro da wanzar da zaman lafiya, irinta ake bukata a daukacin duniya. Yayin taron na Shangri La, kasar Sin ta gabatar da wasu shawarwarin wanzar da tsaro a duniya. Daga cikinsu kuma, akwai kiyaye halaltacciyar moriyar tsaro ta dukkan kasashen duniya. Tabbas, kiyaye moriyar tsaro da cikakken ikon kasashe, abu ne mai muhimmancin gaske, domin rashin hakan shi ke ingiza rikici da tashe-tashen hankula. Duniya ta shaida yadda wasu kasashe ke yi katsalandan cikin harkokin gidan kasashen waje, lamarin da ya kasance babban abun dake haifar da rikice-rikicen da muke gani a yanzu. Wajibi ne kasashen duniya dake kiran kansu manya, su mayar da hankali ga harkokinsu na gida maimakon zuba kudi da bata lokaci wajen ingiza yake-yake a kasashen waje, domin hakan ba zai taba kawo zaman lafiyar da dan Adam ke muradi ba.

Haka kuma, Sin ta ce ya kamata a tabbatar da daidaito da adalci a tsakanin kasa da kasa. Dukkan kasashen duniya manya ko kanana, daya ne, babu wadda ta fi wata. A ganina, rashin girmamawar da wasu manyan kasashe ke yi wa wasu, yana taka muhimmiyar rawa wajen haifar da fitina ko nuna fin karfi ko kuma ta’azzarar rikice-rikice. Ana bukatar garambuwal a harkokin jagorantar duniya domin a rika jin muryoyin kasashe da dama ba wasu ’yan tsiraru kadai ba. Hakan, zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da tsaro da zaman lafiya a duniya, da kuma kare kananan kasashe daga fin karfi da danniya.

Yanayin tsaro dake akwai a kasar Sin, daya ne daga cikin abubuwan da suke burge ni da kasar, kuma na yi imanin idan kasa da kasa za su yi amfani da shawarar kasar Sin, to dan Adam zai kasance cikin kwanciyar hankali, haka kuma za a samu jituwa tsakanin mabanbantan al’ummomi. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Li QiangWang yiXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajj 2024: Jihar Kaduna Ta Kammala Jigilar Maniyyata Fiye Da 4,000 Zuwa Saudiyya 

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

Related

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

44 minutes ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

2 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

3 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

4 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

5 hours ago
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

22 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

'Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Sin

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.