• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kasar Sin Sun Dace Da Bukatun Tabbatar Da Tsaron Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarwarin Kasar Sin Sun Dace Da Bukatun Tabbatar Da Tsaron Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin kammala taro kan tsaro na Shangri-La a Singapore a ranar Lahadi, tawagar kasar Sin ta ce kasar ta tabbatar da kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa bisa ayyukanta masu amfani, ta yadda ta ba da gudummawa wajen samar da tsaron jama’a da kyautata zamantakewar kasa da kasa.

Tabbas salon kasar Sin game da batun tsaro da ma sauran batutuwa, ya fita daban da na sauran kasashen da suka ci gaba, domin ba ta kasance mai tayar da fitina ko takala ko kara rura wutar rikici ba, maimakon haka, ta kasance mai sulhu tsakanin bangarorin da ba sa jituwa, kuma mai kira da a hau teburin tattaunawa da tabbatar da adalci da kuma warware matsaloli tun daga tushe.

  • Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara
  • Ƴan Bindigar Nijeriya Sun Kai Hari Ƙasar Niger

A ko da yaushe ta kan yi la’akari da moriyar da halaltattun hakkokin al’ummomin kasa da kasa, haka kuma ba ta sanya siyasa cikin al’ummarn da suka shafi rayuwar fararen hula. Yanayin zaman lafiya da al’ummar kasar ke morewa, ya isa tabbatar da cewa, hanyar kasar Sin na neman tsaro da wanzar da zaman lafiya, irinta ake bukata a daukacin duniya. Yayin taron na Shangri La, kasar Sin ta gabatar da wasu shawarwarin wanzar da tsaro a duniya. Daga cikinsu kuma, akwai kiyaye halaltacciyar moriyar tsaro ta dukkan kasashen duniya. Tabbas, kiyaye moriyar tsaro da cikakken ikon kasashe, abu ne mai muhimmancin gaske, domin rashin hakan shi ke ingiza rikici da tashe-tashen hankula. Duniya ta shaida yadda wasu kasashe ke yi katsalandan cikin harkokin gidan kasashen waje, lamarin da ya kasance babban abun dake haifar da rikice-rikicen da muke gani a yanzu. Wajibi ne kasashen duniya dake kiran kansu manya, su mayar da hankali ga harkokinsu na gida maimakon zuba kudi da bata lokaci wajen ingiza yake-yake a kasashen waje, domin hakan ba zai taba kawo zaman lafiyar da dan Adam ke muradi ba.

Haka kuma, Sin ta ce ya kamata a tabbatar da daidaito da adalci a tsakanin kasa da kasa. Dukkan kasashen duniya manya ko kanana, daya ne, babu wadda ta fi wata. A ganina, rashin girmamawar da wasu manyan kasashe ke yi wa wasu, yana taka muhimmiyar rawa wajen haifar da fitina ko nuna fin karfi ko kuma ta’azzarar rikice-rikice. Ana bukatar garambuwal a harkokin jagorantar duniya domin a rika jin muryoyin kasashe da dama ba wasu ’yan tsiraru kadai ba. Hakan, zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da tsaro da zaman lafiya a duniya, da kuma kare kananan kasashe daga fin karfi da danniya.

Yanayin tsaro dake akwai a kasar Sin, daya ne daga cikin abubuwan da suke burge ni da kasar, kuma na yi imanin idan kasa da kasa za su yi amfani da shawarar kasar Sin, to dan Adam zai kasance cikin kwanciyar hankali, haka kuma za a samu jituwa tsakanin mabanbantan al’ummomi. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Li QiangWang yiXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajj 2024: Jihar Kaduna Ta Kammala Jigilar Maniyyata Fiye Da 4,000 Zuwa Saudiyya 

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

Related

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

8 minutes ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

1 hour ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

3 hours ago
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

21 hours ago
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
Daga Birnin Sin

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

21 hours ago
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba
Daga Birnin Sin

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

22 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

'Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.