ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kasar Sin Sun Dace Da Bukatun Tabbatar Da Tsaron Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Yayin kammala taro kan tsaro na Shangri-La a Singapore a ranar Lahadi, tawagar kasar Sin ta ce kasar ta tabbatar da kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa bisa ayyukanta masu amfani, ta yadda ta ba da gudummawa wajen samar da tsaron jama’a da kyautata zamantakewar kasa da kasa.

Tabbas salon kasar Sin game da batun tsaro da ma sauran batutuwa, ya fita daban da na sauran kasashen da suka ci gaba, domin ba ta kasance mai tayar da fitina ko takala ko kara rura wutar rikici ba, maimakon haka, ta kasance mai sulhu tsakanin bangarorin da ba sa jituwa, kuma mai kira da a hau teburin tattaunawa da tabbatar da adalci da kuma warware matsaloli tun daga tushe.

  • Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara
  • Ƴan Bindigar Nijeriya Sun Kai Hari Ƙasar Niger

A ko da yaushe ta kan yi la’akari da moriyar da halaltattun hakkokin al’ummomin kasa da kasa, haka kuma ba ta sanya siyasa cikin al’ummarn da suka shafi rayuwar fararen hula. Yanayin zaman lafiya da al’ummar kasar ke morewa, ya isa tabbatar da cewa, hanyar kasar Sin na neman tsaro da wanzar da zaman lafiya, irinta ake bukata a daukacin duniya. Yayin taron na Shangri La, kasar Sin ta gabatar da wasu shawarwarin wanzar da tsaro a duniya. Daga cikinsu kuma, akwai kiyaye halaltacciyar moriyar tsaro ta dukkan kasashen duniya. Tabbas, kiyaye moriyar tsaro da cikakken ikon kasashe, abu ne mai muhimmancin gaske, domin rashin hakan shi ke ingiza rikici da tashe-tashen hankula. Duniya ta shaida yadda wasu kasashe ke yi katsalandan cikin harkokin gidan kasashen waje, lamarin da ya kasance babban abun dake haifar da rikice-rikicen da muke gani a yanzu. Wajibi ne kasashen duniya dake kiran kansu manya, su mayar da hankali ga harkokinsu na gida maimakon zuba kudi da bata lokaci wajen ingiza yake-yake a kasashen waje, domin hakan ba zai taba kawo zaman lafiyar da dan Adam ke muradi ba.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, Sin ta ce ya kamata a tabbatar da daidaito da adalci a tsakanin kasa da kasa. Dukkan kasashen duniya manya ko kanana, daya ne, babu wadda ta fi wata. A ganina, rashin girmamawar da wasu manyan kasashe ke yi wa wasu, yana taka muhimmiyar rawa wajen haifar da fitina ko nuna fin karfi ko kuma ta’azzarar rikice-rikice. Ana bukatar garambuwal a harkokin jagorantar duniya domin a rika jin muryoyin kasashe da dama ba wasu ’yan tsiraru kadai ba. Hakan, zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da tsaro da zaman lafiya a duniya, da kuma kare kananan kasashe daga fin karfi da danniya.

Yanayin tsaro dake akwai a kasar Sin, daya ne daga cikin abubuwan da suke burge ni da kasar, kuma na yi imanin idan kasa da kasa za su yi amfani da shawarar kasar Sin, to dan Adam zai kasance cikin kwanciyar hankali, haka kuma za a samu jituwa tsakanin mabanbantan al’ummomi. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

'Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.