ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Kasar Sin Sun Dace Da Bukatun Tabbatar Da Tsaron Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Yayin kammala taro kan tsaro na Shangri-La a Singapore a ranar Lahadi, tawagar kasar Sin ta ce kasar ta tabbatar da kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa bisa ayyukanta masu amfani, ta yadda ta ba da gudummawa wajen samar da tsaron jama’a da kyautata zamantakewar kasa da kasa.

Tabbas salon kasar Sin game da batun tsaro da ma sauran batutuwa, ya fita daban da na sauran kasashen da suka ci gaba, domin ba ta kasance mai tayar da fitina ko takala ko kara rura wutar rikici ba, maimakon haka, ta kasance mai sulhu tsakanin bangarorin da ba sa jituwa, kuma mai kira da a hau teburin tattaunawa da tabbatar da adalci da kuma warware matsaloli tun daga tushe.

  • Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara
  • Ƴan Bindigar Nijeriya Sun Kai Hari Ƙasar Niger

A ko da yaushe ta kan yi la’akari da moriyar da halaltattun hakkokin al’ummomin kasa da kasa, haka kuma ba ta sanya siyasa cikin al’ummarn da suka shafi rayuwar fararen hula. Yanayin zaman lafiya da al’ummar kasar ke morewa, ya isa tabbatar da cewa, hanyar kasar Sin na neman tsaro da wanzar da zaman lafiya, irinta ake bukata a daukacin duniya. Yayin taron na Shangri La, kasar Sin ta gabatar da wasu shawarwarin wanzar da tsaro a duniya. Daga cikinsu kuma, akwai kiyaye halaltacciyar moriyar tsaro ta dukkan kasashen duniya. Tabbas, kiyaye moriyar tsaro da cikakken ikon kasashe, abu ne mai muhimmancin gaske, domin rashin hakan shi ke ingiza rikici da tashe-tashen hankula. Duniya ta shaida yadda wasu kasashe ke yi katsalandan cikin harkokin gidan kasashen waje, lamarin da ya kasance babban abun dake haifar da rikice-rikicen da muke gani a yanzu. Wajibi ne kasashen duniya dake kiran kansu manya, su mayar da hankali ga harkokinsu na gida maimakon zuba kudi da bata lokaci wajen ingiza yake-yake a kasashen waje, domin hakan ba zai taba kawo zaman lafiyar da dan Adam ke muradi ba.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, Sin ta ce ya kamata a tabbatar da daidaito da adalci a tsakanin kasa da kasa. Dukkan kasashen duniya manya ko kanana, daya ne, babu wadda ta fi wata. A ganina, rashin girmamawar da wasu manyan kasashe ke yi wa wasu, yana taka muhimmiyar rawa wajen haifar da fitina ko nuna fin karfi ko kuma ta’azzarar rikice-rikice. Ana bukatar garambuwal a harkokin jagorantar duniya domin a rika jin muryoyin kasashe da dama ba wasu ’yan tsiraru kadai ba. Hakan, zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da tsaro da zaman lafiya a duniya, da kuma kare kananan kasashe daga fin karfi da danniya.

Yanayin tsaro dake akwai a kasar Sin, daya ne daga cikin abubuwan da suke burge ni da kasar, kuma na yi imanin idan kasa da kasa za su yi amfani da shawarar kasar Sin, to dan Adam zai kasance cikin kwanciyar hankali, haka kuma za a samu jituwa tsakanin mabanbantan al’ummomi. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

'Yan Bindiga Sun Sace Wasu Malaman Jami’a A Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.