• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehun Borno Ya Bukaci Tinubu Ya Kwato Kananan Hukumomin Da Ke Hannun ‘Yan Boko Haram

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Shehun Borno Ya Bukaci Tinubu Ya Kwato Kananan Hukumomin Da Ke Hannun ‘Yan Boko Haram
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar-Ibn Garbai Al-Amin El-Kanemi, ya yi kira ga Shugaban kasa, Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tabbatar da yin duk mai yiyuwa wajen kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram da har yanzu suke rike da shalkwatar karamar hukumar Guzamala da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam, domin bai wa miliyoyin mazauna yankunan da suka yi gudun hijira damar komawa gidajensu na asali.

Shehun Borno ya kuma lura da cewa hanya daya tilo da za a samu dawo da karfin ikon mulkin farar hula a wadannan yankunan da abun ya shafa shi ne, hukumomin tsaro su tashi tsaye su gwabza yaki da ‘yan ta’addan har sai sun amshe iko da yankunan daga hannunsu, musamman a karamar hukumar Guzamala, inda babu wani farin hulan da ke wajen tsawon shekaru.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Basaraken ya shaida hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar barka da sallah ga mai rikon mukamin gwamnan Jihar Borno, Dakta Umar Kadafur a gidan gwamnatin jihar da ke Maiduguri a ranar Lahadi.

LEADERSHIP ta labarto cewa irin wannan rokon ya kuma fito daga bakin kakakin majalisar dokokin Jihar Borno, Hon. Abdulkarim Lawan a lokacin da ke gabatar da sakonsa na ranar tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya na 2024.

Shehun a daidai lokacin da ke yaba wa kokari da sadaukarwar sojojin Nijeriya wajen dawo da martabar zaman lafiya a shiyyar arewa maso gabas da ma Nijeriya baki daya, ya ce, gazawar sojojin kuma wajen kwato yankunan da ke hannun ‘yan Boko Haram ya zama babban damuwa ga iyaye da dama na hanasu zuwa gonakansu da ba su damar nema wa ‘ya’yansu ilimi mai inganci da suke da burin samu. Ya misalta hakan a matsayin babban kalubalen da zai iya kawo cikas ga ci gaban da ake has ashen samu.

Labarai Masu Nasaba

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Sarkin ya ce, “Na zo nan ne ni da mutanena domin taya gwamnati da al’umman Jihar Borno murnar gudanar da shagurgulan babban sallah cikin kwanciyar hankali.

“Ina yaba wa gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, musamman gwamnan Babagana Zulum bisa kokarinsu da suke yi wajen ganin sun yaki ‘yan ta’addan Boko Haram.

“Bugu da kari, bari na yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga Shugaban kasa Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tashi tsaye wajen kawar da ‘yan ta’addan Boko Haram da suka mayaye shalkwatar karamar hukumar Guzamala, da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam domin ganin an samu yanayin da miliyoyin mazauna yankunan za su samu damar komawa gidajensu,” Shehun Borno ya shaida.

Da yake maida jawabi, mai rikon gwamnan jihar, Dakta Kadafur, ya gode wa sarkin bisa wannan ziyarar barka da sallah.

Ya ce tuni aka kafa kwamiti a karkashin jagorancin kwamishinan kula da kananan hukumomi da harkokin masarautu, Hon. Sugum Mai Mele, ya kuma ce gamayyar jami’ar tsaro (MNJTF) suna aiki tukuru wajen ganin sun tabbatar komai ya dawo yadda yake tare da tabbatar da cewa mutanen da suka bar gidajensu a Guzamala sun samu damar komawa gidajensu na asali.

Ya tabbatar da cewa kafin karewar wa’adin gwamnati mai ci kowani dan gudun hijira zai koma gidansa na asali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BornoShehun BornoTinubuTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Labarai

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

2 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

4 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

15 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

16 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

18 hours ago
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.