ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehun Borno Ya Bukaci Tinubu Ya Kwato Kananan Hukumomin Da Ke Hannun ‘Yan Boko Haram

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Shehun Borno

Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar-Ibn Garbai Al-Amin El-Kanemi, ya yi kira ga Shugaban kasa, Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tabbatar da yin duk mai yiyuwa wajen kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram da har yanzu suke rike da shalkwatar karamar hukumar Guzamala da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam, domin bai wa miliyoyin mazauna yankunan da suka yi gudun hijira damar komawa gidajensu na asali.

Shehun Borno ya kuma lura da cewa hanya daya tilo da za a samu dawo da karfin ikon mulkin farar hula a wadannan yankunan da abun ya shafa shi ne, hukumomin tsaro su tashi tsaye su gwabza yaki da ‘yan ta’addan har sai sun amshe iko da yankunan daga hannunsu, musamman a karamar hukumar Guzamala, inda babu wani farin hulan da ke wajen tsawon shekaru.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Basaraken ya shaida hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar barka da sallah ga mai rikon mukamin gwamnan Jihar Borno, Dakta Umar Kadafur a gidan gwamnatin jihar da ke Maiduguri a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta labarto cewa irin wannan rokon ya kuma fito daga bakin kakakin majalisar dokokin Jihar Borno, Hon. Abdulkarim Lawan a lokacin da ke gabatar da sakonsa na ranar tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya na 2024.

Shehun a daidai lokacin da ke yaba wa kokari da sadaukarwar sojojin Nijeriya wajen dawo da martabar zaman lafiya a shiyyar arewa maso gabas da ma Nijeriya baki daya, ya ce, gazawar sojojin kuma wajen kwato yankunan da ke hannun ‘yan Boko Haram ya zama babban damuwa ga iyaye da dama na hanasu zuwa gonakansu da ba su damar nema wa ‘ya’yansu ilimi mai inganci da suke da burin samu. Ya misalta hakan a matsayin babban kalubalen da zai iya kawo cikas ga ci gaban da ake has ashen samu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sarkin ya ce, “Na zo nan ne ni da mutanena domin taya gwamnati da al’umman Jihar Borno murnar gudanar da shagurgulan babban sallah cikin kwanciyar hankali.

“Ina yaba wa gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, musamman gwamnan Babagana Zulum bisa kokarinsu da suke yi wajen ganin sun yaki ‘yan ta’addan Boko Haram.

“Bugu da kari, bari na yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga Shugaban kasa Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tashi tsaye wajen kawar da ‘yan ta’addan Boko Haram da suka mayaye shalkwatar karamar hukumar Guzamala, da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam domin ganin an samu yanayin da miliyoyin mazauna yankunan za su samu damar komawa gidajensu,” Shehun Borno ya shaida.

Da yake maida jawabi, mai rikon gwamnan jihar, Dakta Kadafur, ya gode wa sarkin bisa wannan ziyarar barka da sallah.

Ya ce tuni aka kafa kwamiti a karkashin jagorancin kwamishinan kula da kananan hukumomi da harkokin masarautu, Hon. Sugum Mai Mele, ya kuma ce gamayyar jami’ar tsaro (MNJTF) suna aiki tukuru wajen ganin sun tabbatar komai ya dawo yadda yake tare da tabbatar da cewa mutanen da suka bar gidajensu a Guzamala sun samu damar komawa gidajensu na asali.

Ya tabbatar da cewa kafin karewar wa’adin gwamnati mai ci kowani dan gudun hijira zai koma gidansa na asali.

Shehun Borno
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.