ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehun Borno Ya Bukaci Tinubu Ya Kwato Kananan Hukumomin Da Ke Hannun ‘Yan Boko Haram

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Shehun Borno

Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar-Ibn Garbai Al-Amin El-Kanemi, ya yi kira ga Shugaban kasa, Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tabbatar da yin duk mai yiyuwa wajen kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram da har yanzu suke rike da shalkwatar karamar hukumar Guzamala da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam, domin bai wa miliyoyin mazauna yankunan da suka yi gudun hijira damar komawa gidajensu na asali.

Shehun Borno ya kuma lura da cewa hanya daya tilo da za a samu dawo da karfin ikon mulkin farar hula a wadannan yankunan da abun ya shafa shi ne, hukumomin tsaro su tashi tsaye su gwabza yaki da ‘yan ta’addan har sai sun amshe iko da yankunan daga hannunsu, musamman a karamar hukumar Guzamala, inda babu wani farin hulan da ke wajen tsawon shekaru.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Basaraken ya shaida hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar barka da sallah ga mai rikon mukamin gwamnan Jihar Borno, Dakta Umar Kadafur a gidan gwamnatin jihar da ke Maiduguri a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta labarto cewa irin wannan rokon ya kuma fito daga bakin kakakin majalisar dokokin Jihar Borno, Hon. Abdulkarim Lawan a lokacin da ke gabatar da sakonsa na ranar tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya na 2024.

Shehun a daidai lokacin da ke yaba wa kokari da sadaukarwar sojojin Nijeriya wajen dawo da martabar zaman lafiya a shiyyar arewa maso gabas da ma Nijeriya baki daya, ya ce, gazawar sojojin kuma wajen kwato yankunan da ke hannun ‘yan Boko Haram ya zama babban damuwa ga iyaye da dama na hanasu zuwa gonakansu da ba su damar nema wa ‘ya’yansu ilimi mai inganci da suke da burin samu. Ya misalta hakan a matsayin babban kalubalen da zai iya kawo cikas ga ci gaban da ake has ashen samu.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sarkin ya ce, “Na zo nan ne ni da mutanena domin taya gwamnati da al’umman Jihar Borno murnar gudanar da shagurgulan babban sallah cikin kwanciyar hankali.

“Ina yaba wa gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, musamman gwamnan Babagana Zulum bisa kokarinsu da suke yi wajen ganin sun yaki ‘yan ta’addan Boko Haram.

“Bugu da kari, bari na yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga Shugaban kasa Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tashi tsaye wajen kawar da ‘yan ta’addan Boko Haram da suka mayaye shalkwatar karamar hukumar Guzamala, da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam domin ganin an samu yanayin da miliyoyin mazauna yankunan za su samu damar komawa gidajensu,” Shehun Borno ya shaida.

Da yake maida jawabi, mai rikon gwamnan jihar, Dakta Kadafur, ya gode wa sarkin bisa wannan ziyarar barka da sallah.

Ya ce tuni aka kafa kwamiti a karkashin jagorancin kwamishinan kula da kananan hukumomi da harkokin masarautu, Hon. Sugum Mai Mele, ya kuma ce gamayyar jami’ar tsaro (MNJTF) suna aiki tukuru wajen ganin sun tabbatar komai ya dawo yadda yake tare da tabbatar da cewa mutanen da suka bar gidajensu a Guzamala sun samu damar komawa gidajensu na asali.

Ya tabbatar da cewa kafin karewar wa’adin gwamnati mai ci kowani dan gudun hijira zai koma gidansa na asali.

Shehun Borno
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.