ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehun Borno Ya Bukaci Tinubu Ya Kwato Kananan Hukumomin Da Ke Hannun ‘Yan Boko Haram

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Shehun Borno

Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar-Ibn Garbai Al-Amin El-Kanemi, ya yi kira ga Shugaban kasa, Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tabbatar da yin duk mai yiyuwa wajen kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram da har yanzu suke rike da shalkwatar karamar hukumar Guzamala da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam, domin bai wa miliyoyin mazauna yankunan da suka yi gudun hijira damar komawa gidajensu na asali.

Shehun Borno ya kuma lura da cewa hanya daya tilo da za a samu dawo da karfin ikon mulkin farar hula a wadannan yankunan da abun ya shafa shi ne, hukumomin tsaro su tashi tsaye su gwabza yaki da ‘yan ta’addan har sai sun amshe iko da yankunan daga hannunsu, musamman a karamar hukumar Guzamala, inda babu wani farin hulan da ke wajen tsawon shekaru.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Basaraken ya shaida hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar barka da sallah ga mai rikon mukamin gwamnan Jihar Borno, Dakta Umar Kadafur a gidan gwamnatin jihar da ke Maiduguri a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta labarto cewa irin wannan rokon ya kuma fito daga bakin kakakin majalisar dokokin Jihar Borno, Hon. Abdulkarim Lawan a lokacin da ke gabatar da sakonsa na ranar tunawa da samun ‘yancin kan Nijeriya na 2024.

Shehun a daidai lokacin da ke yaba wa kokari da sadaukarwar sojojin Nijeriya wajen dawo da martabar zaman lafiya a shiyyar arewa maso gabas da ma Nijeriya baki daya, ya ce, gazawar sojojin kuma wajen kwato yankunan da ke hannun ‘yan Boko Haram ya zama babban damuwa ga iyaye da dama na hanasu zuwa gonakansu da ba su damar nema wa ‘ya’yansu ilimi mai inganci da suke da burin samu. Ya misalta hakan a matsayin babban kalubalen da zai iya kawo cikas ga ci gaban da ake has ashen samu.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Sarkin ya ce, “Na zo nan ne ni da mutanena domin taya gwamnati da al’umman Jihar Borno murnar gudanar da shagurgulan babban sallah cikin kwanciyar hankali.

“Ina yaba wa gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, musamman gwamnan Babagana Zulum bisa kokarinsu da suke yi wajen ganin sun yaki ‘yan ta’addan Boko Haram.

“Bugu da kari, bari na yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga Shugaban kasa Bola Tinubu da hukumomin tsaro da su tashi tsaye wajen kawar da ‘yan ta’addan Boko Haram da suka mayaye shalkwatar karamar hukumar Guzamala, da wasu kauyuka da ke Kukawa, karamar hukumar Abadam domin ganin an samu yanayin da miliyoyin mazauna yankunan za su samu damar komawa gidajensu,” Shehun Borno ya shaida.

Da yake maida jawabi, mai rikon gwamnan jihar, Dakta Kadafur, ya gode wa sarkin bisa wannan ziyarar barka da sallah.

Ya ce tuni aka kafa kwamiti a karkashin jagorancin kwamishinan kula da kananan hukumomi da harkokin masarautu, Hon. Sugum Mai Mele, ya kuma ce gamayyar jami’ar tsaro (MNJTF) suna aiki tukuru wajen ganin sun tabbatar komai ya dawo yadda yake tare da tabbatar da cewa mutanen da suka bar gidajensu a Guzamala sun samu damar komawa gidajensu na asali.

Ya tabbatar da cewa kafin karewar wa’adin gwamnati mai ci kowani dan gudun hijira zai koma gidansa na asali.

Shehun Borno
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 5, 2026
Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
Labarai

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
Labarai

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 5, 2026
Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

July 5, 2026
Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

July 5, 2026
Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.